< 2 Samuel 17 >

1 Then Ahithophel said to Absalom: “I will choose for myself twelve thousand men, and rising up, I will pursue David this night.
Ahitofel ya ce wa Absalom, “Zan zaɓi mutum dubu goma sha biyu su fita a daren nan in fafari Dawuda.
2 And rushing against him, for he is weary and has weakened hands, I will strike him. And when all the people who are with him will have fled, I will strike down the king in isolation.
Zan fāɗa masa sa’ad da yake cikin gajiya da karayar zuciya. Zan firgita shi, mutanen da suke tare da shi kuwa za su gudu. Sarki ne kaɗai zan kashe
3 And I will lead back the entire people, returning in the manner of one man. For you are seeking only one man. And all the people shall be in peace.”
in dawo da dukan mutanen a gare ka. Mutuwar wanda kake nema zai zama dawowar duka; dukan mutanen ba za su cutu ba.”
4 And this word pleased Absalom and all those greater by birth of Israel.
Wannan shawara ta gamshi Absalom da dukan dattawan Isra’ila.
5 But Absalom said, “Summon Hushai the Archite, and let us hear what he also may say.”
Amma Absalom ya ce, “A kira mini Hushai mutumin Arkitawan nan shi ma, mu ji abin da zai ce.”
6 And when Hushai had gone to Absalom, Absalom said to him: “Ahithophel has spoken a word in this manner. Should we do it or not? What counsel do you give?”
Da Hushai ya zo wurinsa, sai Absalom ya ce, “Ahitofel ya ba da wannan shawara. Mu yi abin da ya ce? In ba haka ba, sai ka ba mu ra’ayinka.”
7 And Hushai said to Absalom, “The counsel that Ahithophel has given at this time is not good.”
Hushai ya ce wa Absalom, “Shawarar da Ahitofel ya bayar a wannan lokaci kam, ba ta da kyau.
8 And again Hushai declared, “You know your father, and the men who are with him, to be very strong and bitter in soul, comparable to a bear raging in the forest when her young have been taken away. Moreover, your father is a man of war, and so he will not live among the people.
Ka san mahaifinka da mutanensa mayaƙa ne, suna cikin fushi kamar mugun beyar da aka ƙwace mata’ya’ya. Ban da haka ma, mahaifinka gogagge ne a yaƙi; ba zai kwana da rundunar ba.
9 Perhaps now he hides in pits, or in another place, wherever he wills. And if by chance, in the beginning, anyone may fall, whoever hears about it, no matter what he has heard, will say, ‘There is a slaughter among the people who were following Absalom.’
Kai, ko yanzu ma, ya riga ya ɓuya cikin kogo ko kuma a wani wuri. In har ya fara kai wa rundunarka hari duk wanda ya ji, zai ce, ‘An yi kaca-kaca da rundunar da suka bi Absalom.’
10 And even the very strong, whose heart is like the heart of a lion, will be weakened out of fear. For all the people of Israel know your father to be a valiant man, and that all who are with him are robust.
Kai, ko jarumi mai zuciya kamar na zaki ma, zai narke don tsoro, gama dukan Isra’ila sun sani mahaifinka mayaƙi ne, sun kuma san cewa waɗanda suke tare da shi jarumawa ne.
11 But this seems to me to be the right counsel: Let all of Israel be gathered to you, from Dan to Beersheba, like the sand of the sea which is innumerable. And you will be in their midst.
“Saboda haka ina ba ka shawara, bari a tara maka dukan Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba da yawansu ya yi kamar yashin bakin teku, kai kanka ka jagorance su zuwa fagen fama.
12 And we shall rush against him in whatever place he will have been found. And we shall cover him, as the dew usually falls upon the ground. And we shall not leave behind even one of the men who are with him.
Sa’an nan za mu fāɗa masa duk inda yake, za mu fāɗa masa kamar yadda raɓa takan fāɗo a bisa ƙasa. Da shi da mutanensa babu ko ɗaya da za a bari da rai.
13 And if he will enter into any city, all of Israel shall encircle that city with ropes. And we will pull it into the torrent, so that there may not be found even one small stone from it.”
In ma ya janye zuwa cikin birni, sai dukan Isra’ila su kawo igiyoyi wa wannan birni, su ja shi zuwa kwari yă wargaje, yadda ba za a bar wani dutse a kan wani ba.”
14 And Absalom, with all the men of Israel, said: “The counsel of Hushai the Archite is better than the counsel of Ahithophel.” So, by an act of the Lord, the useful counsel of Ahithophel was defeated, in order that the Lord might lead evil over Absalom.
Absalom da dukan mutanen Isra’ila suka ce, “Shawarar Hushai mutumin Arkitawa ta fi ta Ahitofel kyau.” Gama Ubangiji ya ƙudura yă wofinta kyakkyawar shawarar Ahitofel, don yă jawo wa Absalom masifa.
15 And Hushai said to the priests, Zadok and Abiathar: “Ahithophel gave counsel to Absalom and to the elders of Israel in this and that manner. And I gave counsel in such and such a manner.
Hushai ya ce wa Zadok da Abiyatar, firistoci, “Ahitofel ya ba wa Absalom da dattawan Isra’ila shawara su yi kaza da kaza, amma na ba su shawara su yi haka, su yi haka.
16 Now therefore, send quickly, and report to David, saying: ‘You shall not stay this night in the plains of the desert. Instead, without delay, go across. Otherwise the king may be engulfed, and all the people who are with him.’”
Yanzu sai ku aika wa Dawuda saƙo nan da nan ku ce masa, ‘Kada ka kwana a mashigai cikin hamada; ka tabbata ka haye ba faci, in ba haka ba sarki da dukan mutanensa za su hallaka.’”
17 But Jonathan and Ahimaaz remained beside the Fountain of Rogel. And a handmaid went away and reported it to them. And they set out, so that they might carry the report to king David. For they could not be seen, nor enter into the city.
Yonatan da Ahimawaz suna zaune a En Rogel. Wata baranya ce za tă je ta faɗa musu, su kuma su tafi su gaya wa Sarki Dawuda don suna tsoro kada a ga suna shiga birnin.
18 But a certain young man saw them, and he revealed it to Absalom. Yet truly, they traveled quickly and entered into the house of a certain man in Bahurim, who had a well in his court, and they descended into it.
Amma wani saurayi ya gan su, ya gaya wa Absalom. Sai dukansu biyu suka tashi da sauri suka shiga gidan wani mutum a Bahurim. Yana da rijiya a cikin gida, sai suka shiga cikinta.
19 Then a woman took and spread a covering over the mouth of the well, as if drying hulled barley. And so the matter was hidden.
Matarsa mutumin kuwa ta kawo tabarma ta shimfiɗa a bakin rijiyar, sai ta kawo hatsi ta baza a kanta. Ba kuwa wanda ya san abin da ta yi.
20 And when the servants of Absalom had entered into the house, they said to the woman, “Where is Ahimaaz and Jonathan?” And the woman responded to them, “They passed through hurriedly, after they had taken a little water.” But those who were seeking them, when they had not found them, returned to Jerusalem.
Da mutanen Absalom suka zo wurin matan a gidan, suka ce, “Ina Yonatan da Ahimawaz?” Matar ta ce, “Tuni, sun haye rafi.” Sai mutanen suka yi ta nemansu amma ba su ga kowa, sai suka koma Urushalima.
21 And when they had gone, they ascended from the well. And traveling, they reported to king David, and they said: “Rise up, and go across the river quickly. For Ahithophel has given a counsel of this kind against you.”
Bayan mutanen suka tafi, sai su biyun suka fito daga rijiyar suka je suka gaya wa Sarki Dawuda. Suka ce masa, “Maza ka ƙetare kogi; Ahitofel ya ba wa Absalom shawara a yi maka kaza da kaza.”
22 Therefore, David rose up, and all the people who were with him, and they crossed over the Jordan, until first light. And not even one of them was left behind who had not crossed over the river.
Saboda haka Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka tashi suka ƙetare Urdun. Kafin wayewar gari, babu wanda ya rage da bai haye ba.
23 Then Ahithophel, seeing that his counsel had not been done, saddled his donkey, and he rose up and went away to his own house and to his own city. And putting his house in order, he killed himself by hanging. And he was buried in the sepulcher of his father.
Da Ahitofel ya ga ba a bi shawararsa ba, sai ya hau jakinsa ya koma gidansa a garinsu. Ya kintsa gidansa sa’an nan ya rataye kansa. Ta haka ya mutu, aka kuma binne shi a kabarin mahaifinsa.
24 Then David went to the encampment, and Absalom crossed over the Jordan, he and all the men of Israel with him.
Dawuda kuwa ya tafi Mahanayim. Absalom kuma ya ƙetare Urdun tare da dukan mutanen Isra’ila.
25 Truly, Absalom appointed Amasa in place of Joab over the army. Now Amasa was the son of a man who was called Ithra of Jezrael, who entered to Abigail, the daughter of Nahash, the sister of Zeruiah, who was the mother of Joab.
Absalom ya riga ya naɗa Amasa a kan sojoji a maimakon Yowab. Amasa kuwa ɗan wani mutum mai suna Itra ne, mutumin Ishmayel wanda ya auri Abigiyel,’yar Nahash,’yar’uwar Zeruhiya mahaifiyar Yowab.
26 And Israel made camp with Absalom in the land of Gilead.
Isra’ilawa da Absalom suka kafa sansani a ƙasar Gileyad.
27 And when David had arrived at the encampment, Shobi, the son of Nahash, from Rabbah, of the sons of Ammon, and Machir, the son of Ammiel of Lodebar, and Barzillai, the Gileadite of Rogelim,
Sa’ad da Dawuda ya zo Mahanayim, sai Shobi ɗan Nahash daga Rabba ta Ammonawa, da Makir ɗan Ammiyel daga Lo Debar, da Barzillai mutumin Gileyad daga Rogelim
28 brought to him bedding, and tapestries, and earthen vessels, and wheat, and barley, and meal, and cooked grain, and beans, and lentils, and fried chick peas,
suka kawo wa Dawuda da mutanensa tabarmai, da kwanoni, da kayayyakin da aka yi da yumɓu. Suka kuma kawo alkama da sha’ir, da gari, da soyayyen hatsi, da wake, da waken barewa,
29 and honey, and butter, sheep and fattened calves. And they gave these to David and to the people who were with him to eat. For they suspected that the people were faint with hunger and thirst in the desert.
da zuma, da kindirmo, da tumaki, da cukun madarar shanu wa Dawuda da mutanensa su ci. Gama sun ce, “Mutanen suna jin yunwa, sun kuma gaji, ga ƙishirwa a hamada.”

< 2 Samuel 17 >