< 2 Kings 3 >

1 Truly, Joram, the son of Ahab, reigned over Israel, in Samaria, in the eighteenth year of Jehoshaphat, the king of Judah. And he reigned for twelve years.
Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
2 And he did evil in the sight of the Lord, but not as his father and mother did. For he took away the statues of Baal, which his father had made.
Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
3 Yet truly, he did adhere to the sins of Jeroboam, the son of Nebat, who caused Israel to sin; neither did he withdraw from these.
Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
4 Now Mesha, the king of Moab, raised many sheep. And he repaid to the king of Israel one hundred thousand lambs, and one hundred thousand rams, with their fleece.
Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
5 And when Ahab had died, he transgressed the pact that he had with the king of Israel.
Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
6 Therefore, king Joram departed on that day from Samaria, and he took a count of all of Israel.
To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
7 And he sent to Jehoshaphat, the king of Judah, saying: “The king of Moab has withdrawn from me. Come to battle with me against him.” And he responded: “I will go up. What is mine, is yours. My people are your people. And my horses are your horses.”
Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
8 And he said, “Along which way shall we ascend?” So he responded, “Along the desert of Idumea.”
Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
9 Therefore, the king of Israel, and the king of Judah, and the king of Idumea, traveled, and they went by a circuitous path for seven days. But there was no water for the army or for the beasts of burden which were following them.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
10 And the king of Israel said: “Alas, alas, alas! The Lord has gathered we three kings, so that he might deliver us into the hands of Moab.”
Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
11 And Jehoshaphat said, “Is there not a prophet of the Lord here, so that we may appeal to the Lord through him?” And one of the servants of the king of Israel responded, “Elisha, the son of Shaphat, is here, who poured water upon the hands of Elijah.”
Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
12 And Jehoshaphat said, “The word of the Lord is with him.” And so, the king of Israel, with Jehoshaphat, the king of Judah, and with the king of Idumea, descended to him.
Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
13 Then Elisha said to the king of Israel: “What is there between you and me? Go to the prophets of your father and your mother.” And the king of Israel said to him, “Why has the Lord gathered these three kings, so that he might deliver them into the hands of Moab?”
Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
14 And Elisha said to him: “As the Lord of hosts lives, in whose sight I stand, if I was not humbled by the face of Jehoshaphat, the king of Judah, certainly I would neither have listened to you, nor have looked upon you.
Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
15 But now, bring a musician to me.” And while the musician was playing, the hand of the Lord fell upon him, and he said:
Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
16 “Thus says the Lord: Make, in the channel of this torrent, pit after pit.
ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
17 For thus says the Lord: You shall not see wind or rain. And yet this channel shall be filled with water. And you shall drink, you and your families, and your beasts of burden.
Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
18 And this is small in the sight of the Lord. So, in addition, he will also deliver Moab into your hands.
Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
19 And you shall strike every fortified town and every elect city. And you shall cut down every fruitful tree. And you shall obstruct all the sources of water. And you shall cover every excellent field with stones.”
Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
20 Then it happened that, in the morning, when the sacrifices were usually to be offered, behold, water was arriving along the way of Idumea, and the land was filled with water.
Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
21 Then all the Moabites, hearing that the kings had ascended so that they might fight against them, gathered all who had been girded with a belt around them, and they stood at the borders.
To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
22 And rising up in early morning, and when the sun was now rising before the waters, the Moabites saw the waters opposite them, which were red like blood.
Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
23 And they said: “It is the blood of the sword! The kings have fought among themselves, and they have slain one another. Go now, Moab, to the spoils!”
Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
24 And they went into the camp of Israel. But Israel, rising up, struck Moab, and they fled before them. And since they had prevailed, they went and struck down Moab.
Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
25 And they destroyed the cities. And they filled up every excellent field, each one casting stones. And they obstructed all the sources of water. And they cut down all the fruitful trees, to such an extent that only brick walls remained. And the city was encircled by the slingers of stones. And a great part of it was struck down.
Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
26 And when the king of Moab had seen this, specifically, that the enemies had prevailed, he took with him seven hundred men who draw the sword, so that he might break through to the king of Idumea. But they were unable.
Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
27 And taking his firstborn son, who would have reigned in his place, he offered him as a holocaust upon the wall. And there was great indignation in Israel. And they promptly withdrew from him, and they turned back to their own land.
Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.

< 2 Kings 3 >