< 2 Kings 23 >

1 And they reported to the king what she had said. And he sent, and all the elders of Judah and Jerusalem were gathered to him.
Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
2 And the king ascended to the temple of the Lord. And with him were all the men of Judah and all who were living in Jerusalem: the priests, and the prophets, and all the people, from the small to the great. And in the hearing of everyone, he read all the words of the book of the covenant, which was found in the house of the Lord.
Sai ya haura zuwa cikin haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, da na Urushalima, da firistoci, da annabawa, dukan mutane, manya da ƙanana. Ya karanta musu duk kalmomin Littafin Alkawari, wanda aka samu a haikalin Ubangiji.
3 And the king stood upon the step. And he struck a covenant before the Lord, so that they would walk after the Lord, and keep his precepts and testimonies and ceremonies, with all their heart and with all their soul, and so that they would carry out the words of this covenant, which had been written in that book. And the people agreed to the covenant.
Sarki ya tsaya dab da ginshiƙi ya kuma sabunta alkawarin a gaban Ubangiji, ya ce zai bi Ubangiji, yă kiyaye dokokinsa, da ƙa’idodinsa, da farillansa, da dukan zuciyarsa da dukan ransa, ta haka ya tabbatar da kalmomin alkawarin da yake a rubuce a cikin littafin nan. Sa’an nan dukan mutane ma suka yi alkawari yin haka.
4 And the king instructed Hilkiah, the high priest, and the priests of the second order, and the doorkeepers, so that they would cast out of the temple of the Lord all the vessels which had been made for Baal, and for the sacred grove, and for the entire army of heaven. And he burned them outside of Jerusalem, in the steep valley of Kidron. And he carried their dust into Bethel.
Sai Yosiya ya umarci Hilkiya babban firist, tare da firistocin da suke taimakonsa, da masu tsaron ƙofa su kawar da dukan abubuwan da aka yi domin Ba’al, da domin Ashera, da kuma domin dukan rundunar taurari, daga haikalin Ubangiji. Ya ƙone su a bayan Urushalima a filayen Kwarin Kidron, ya kwashe tokan zuwa Betel.
5 And he destroyed the soothsayers, whom the kings of Judah had appointed to sacrifice in the high places throughout the cities of Judah, and all around Jerusalem, along with those who were burning incense to Baal, and to the Sun, and to the Moon, and to the twelve signs, and to the entire army of heaven.
Ya kawar da firistocin gumakan da sarakunan Yahuda suka naɗa don su ƙona turare a masujadan kan tuddai na garuruwan Yahuda, da kuma waɗanda suke kewaye da Urushalima, masu ƙona turare wa Ba’al, rana da wata, ga rukunin taurari, da kuma ga dukan rundunan taurari.
6 And he caused the sacred grove to be carried away from the house of the Lord, outside of Jerusalem, to the steep valley of Kidron. And he burned it there, and reduced it to dust. And he cast the dust over the graves of the common people.
Ya ɗauke ginshiƙin Ashera daga haikalin Ubangiji zuwa Kwarin Kidron can bayan Urushalima, ya ƙone shi a can. Ya niƙa shi sai da ya zama toka, sai ya watsar da ƙurar a filin kabarin talakawa.
7 Also, he destroyed the small places of the effeminate, which were in the house of the Lord, for which the women were weaving something like little houses in the sacred grove.
Ya kuma rurrushe mazaunan karuwai mazan haikali waɗanda suke a haikalin Ubangiji, da kuma inda mata suke yi wa Ashera saƙa.
8 And he gathered together all the priests from the cities of Judah. And he defiled the high places, where the priests were sacrificing, from Geba as far as Beersheba. And he tore down the altars of the gates at the entrance to the gate of Joshua, the leader of the city, which was to the left of the gate of the city.
Yosiya ya kawo dukan firistoci daga garuruwan Yahuda, ya kuma lalatar da masujadan kan tuddai daga Geba har zuwa Beyersheba, inda firistoci suke ƙona turare. Ya rurrushe matsafai a ƙofofi shigan gari na mashigi zuwa Ƙofar Yoshuwa, gwamnan birnin, wanda yake a hagu da ƙofar birnin.
9 Yet truly, the priests of the high places did not ascend to the altar of the Lord in Jerusalem. For they would only eat from the unleavened bread in the midst of their brothers.
Ko da yake firistocin masujadan kan tuddai ba su yi hidima a bagaden Ubangiji a Urushalima ba, sun ci burodi marar yisti tare da sauran firistoci.
10 Also, he defiled Topheth, which is in the steep valley of the son of Hinnom, so that no one would consecrate his son or his daughter, through fire, to Molech.
Ya lalatar da Tofet, wanda yake a Kwarin Ben Hinnom, don kada kowa yă iya yin amfani da wurin don yă miƙa hadayar ɗansa, ko’yarsa a wuta ga Molek.
11 Also, he took away the horses that the kings of Judah had given to the Sun, at the entrance to the temple of the Lord, beside the hallway of Nathan-melech, the eunuch, who was in Pharurim. And he burned the chariots of the Sun with fire.
Ya kawar da dawakan nan da sarakunan Yahuda suka keɓe wa gumakan nan na rana daga mashigin haikalin Ubangiji. Waɗannan dawakan suna kusa da ɗakin Natan Melek, ɗaya daga cikin dattawan sarki. Yosiya ya kuma ƙone kekunan yaƙi a yin sujada ga gumakan nan rana.
12 Also, the altars which were upon the roof of the upper room of Ahaz, which the kings of Judah had made, and the altars which Manasseh had made in the two courts of the temple of the Lord, the king destroyed. And he hurried from there, and he scattered their ashes into the torrent Kidron.
Ya rushe bagadan da sarakunan Yahuda suka kafa a kan ɗakin sama kusa da ɗakin sama na Ahaz, da kuma bagadai biyu da Manasse ya gina a filaye biyu na haikalin Ubangiji. Ya kawar da su daga can, ya farfashe su, ya zubar da tarkacen a Kwarin Kidron.
13 Also, the high places which were in Jerusalem, to the right side of the Mount of Offense, which Solomon, the king of Israel, had built to Ashtoreth, the idol of the Sidonians, and to Chemosh, the offense of Moab, and to Milcom, the abomination of the sons of Ammon, the king defiled.
Sarkin kuma ya lalatar da masujadan kan tuddan da suke gabas da Urushalima, kudu da Tudun Hallaka, waɗanda Solomon sarkin Isra’ila ya gina don Ashtarot, ƙazantacciyar alliyar Sidoniyawa, da Kemosh ƙazantaccen allah na Mowab, da kuma Molek allahn banƙyama na mutanen Ammon.
14 And he crushed the statues, and he cut down the sacred groves. And he filled their places with the bones of the dead.
Yosiya ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya rurrushe ginshiƙan Asheransu, ya baza ƙasusuwan mutane a can.
15 Then too, the altar which was in Bethel, and the high place which Jeroboam, the son of Nebat, who caused Israel to sin, had made: both that altar and the high place he tore down, and burned, and reduced to dust. And then he also set fire to the sacred grove.
Har ma da bagaden Betel, masujadan kan tudun da Yerobowam ɗan Nebat ya yi, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi. Wannan bagade da masujadan kan tudun ma ya kawar, ya ƙone masujadan kan tudun, ya niƙa su, ya kuma ƙone ginshiƙin Ashera.
16 And in that place Josiah, turning, saw the sepulchers which were on the mount. And he sent and took the bones from the sepulchers. And he burned them upon the altar, and he defiled it in accord with the word of the Lord, which was spoken by the man of God, who had predicted these events.
Da Yosiya ya dubi kewaye da shi, ya ga kaburburan da suke can a gefen tudu, sai ya sa aka kwaso ƙasusuwan da suke cikinsu aka ƙone a kan bagade don yă lalatar da shi bisa ga maganar Ubangiji ta bakin mutumin Allah, wanda ya yi annabcin waɗannan abubuwa.
17 And he said, “What is that monument that I see?” And the citizens of that city responded to him: “It is the sepulcher of the man of God, who came from Judah, and who predicted these events, which you have carried out concerning the altar of Bethel.”
Sarkin ya yi tambaya, ya ce, “Wane kabari ke nan nake gani?” Mutanen birnin suka ce, “Ai, kabarin annabin Allah ne wanda ya fito daga Yahuda, shi ne ya yi annabcin waɗannan abubuwan da ka aikata gāba da bagaden Betel.”
18 And he said: “Permit him. Let no one move his bones.” And his bones have remained untouched, with the bones of the prophet who had arrived from Samaria.
Sai ya ce, “Ku rabu da shi, kada wani yă dami ƙasusuwansa.” Saboda haka suka bar kasusuwansa, da na annabin da ya fito Samariya.
19 Then too, all the shrines of the high places, which were in the cities of Samaria, which the kings of Israel had made to provoke the Lord, Josiah took away. And he acted toward them according to all the works that he had done in Bethel.
Kamar yadda ya yi a Betel, Yosiya ya kawar da dukan ɗakunan gumaka a kan tuddan da sarakunan Isra’ila suka gina a garuruwan Samariya, waɗanda suka tozarta Ubangiji.
20 And all the priests of the high places, who were in that place, he killed upon the altars. And he burned the bones of the men upon them. And he returned to Jerusalem.
Yosiya ya yayyanka dukan firistoci na waɗannan masujadan kan tuddai, ya kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kansu. Sa’an nan ya koma Urushalima.
21 And he instructed all the people, saying: “Keep the Passover to the Lord your God, according to what has been written in the book of this covenant.”
Sarkin ya ba da umarnin nan ga dukan mutane, cewa, “Ku yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku, yadda aka rubuta a Littafin Alkawari.”
22 Now no similar Passover was kept, from the days of the judges, who judged Israel, and from all the days of the kings of Israel and the kings of Judah,
Ba a taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa haka ba, tun zamanin da masu shari’a suke aiki a matsayin sarakuna, ko a kwanakin sarakunan Isra’ila, ko na Yahuda.
23 as this Passover, which was kept to the Lord in Jerusalem, in the eighteenth year of king Josiah.
Amma a shekara ta goma sha takwas ta mulkin sarki Yosiya, aka yi Bikin Ƙetarewan nan ga Ubangiji a Urushalima.
24 Then too, Josiah took away those who divined by spirits, and the soothsayers, and the images of the idols, and the defilements, and the abominations, which had been in the land of Judah and Jerusalem, so that he might establish the words of the law, which were written in the book, which Hilkiah, the priest, found in the temple of the Lord.
Ban da haka, Yosiya ya kawar da masu duba, da masu maita, da allolin gidaje, da gumaka, da duk wani abin banƙyaman da ya gani a Yahuda da Urushalima. Ya yi wannan domin yă cika wa’adodin shari’a yadda suke a littafin da Hilkiya firist ya samu a haikalin Ubangiji.
25 There was no king before him similar to him, who returned to the Lord with all his heart, and with all his soul, and with all his strength, in accord with the entire law of Moses. And after him, there rose up no one similar to him.
Babu wani sarki kafin Yosiya, ko kuma a bayansa, wanda ya juya ga Ubangiji da dukan zuciyarsa, da dukan ransa, da dukan ƙarfinsa bisa ga shari’ar Musa, kamar yadda ya yi.
26 Yet truly, the Lord did not turn away from the wrath of his great fury, his fury which was enraged against Judah because of the provocations by which Manasseh had provoked him.
Duk da haka, Ubangiji bai huce daga zafin fushinsa wanda ya ƙuna game da Yahuda saboda abin da Manasse ya aikata don yă tozarta shi ba.
27 And so the Lord said: “And now I will remove Judah from my face, just as I removed Israel. And I will cast aside this city, Jerusalem, which I have chosen, and the house, about which I said: My name shall be there.”
Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan shafe Yahuda ma kamar yadda na shafe Isra’ila, daga gabana, zan ƙi Urushalima birnin da na zaɓa, da wannan haikali wanda na ce, ‘A can Sunana zai kasance.’”
28 Now the rest of the words of Josiah, and all that he did, have these not been written in the book of the words of the days of the kings of Judah?
Game da sauran ayyukan mulkin Yosiya, da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
29 During his days, Pharaoh Neco, the king of Egypt, ascended against the king of the Assyrians to the river Euphrates. And king Josiah went out to meet him. And when he had seen him, he was killed at Megiddo.
Yayinda Yosiya yake sarki, Fir’auna Neko, sarkin Masar ya haura zuwa Kogin Yuferites don yă taimaki sarkin Assuriya da yaƙi. Sarki Yosiya kuwa ya yi ƙoƙari ya hana shi wucewa, sa’ad da Fir’auna Neko ya gan shi, sai ya kashe shi a filin yaƙi a Megiddo.
30 And his servants carried him dead from Megiddo. And they took him to Jerusalem, and they buried him in his own sepulcher. And the people of the land took Jehoahaz, the son of Josiah. And they anointed him, and made him king in place of his father.
Bayin Yosiya suka ɗauko gawarsa daga Megiddo suka kai Urushalima, suka binne shi a kabarinsa. Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa.
31 Jehoahaz was twenty-three years old when he had begun to reign, and he reigned for three months in Jerusalem. The name of his mother was Hamutal, the daughter of Jeremiah, from Libnah.
Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki. Ya yi mulki na wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
32 And he did evil before the Lord, according to all that his fathers had done.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda kakanninsa suka yi.
33 And Pharaoh Neco bound him at Riblah, which is in the land of Hamath, so that he would not reign in Jerusalem. And he imposed a penalty on the land: one hundred talents of silver, and one talent of gold.
Fir’auna Neko ya sa shi a sarƙa a Ribla a ƙasar Hamat don kada yă yi mulki a Urushalima, sa’an nan ya sa wa Yahuda harajin talenti ɗari na azurfa, da talenti ɗaya na zinariya.
34 And Pharaoh Neco appointed Eliakim, the son of Josiah, as king in place of Josiah his father. And he changed his name to Jehoiakim. Then he took Jehoahaz away, and he brought him into Egypt, and there he died.
Fir’auna Neko ya naɗa Eliyakim ɗan Yosiya sarki a maimakon mahaifinsa, ya kuma canja masa suna zuwa Yehohiyakim. Ya ɗauki Yehoyahaz ya kai Masar, a can ya mutu.
35 Now Jehoiakim gave silver and gold to Pharaoh, when he had taxed the land, according to each one who would contribute by the command of Pharaoh. And he exacted both silver and gold from the people of the land, from each one according to his ability, so that he would give to Pharaoh Neco.
Yehohiyakim ya riƙa biyan Fir’auna Neko azurfa da zinariyar da ya umarta. Don yă yi haka sai ya riƙa karɓar azurfa da zinariya daga mutanen ƙasar, kowa bisa ga ƙarfinsa.
36 Jehoiakim was twenty-five years old when he had begun to reign, and he reigned for eleven years in Jerusalem. The name of his mother was Zebidah, the daughter of Pedaiah, from Rumah.
Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Zebuda’yar Fedahiya, mutuniyar Ruma.
37 And he did evil before the Lord, in accord with all that his fathers had done.
Ya kuma aika mugunta a gaban Ubangiji yadda kakanninsa suka yi.

< 2 Kings 23 >