< 2 Chronicles 34 >

1 Josiah was eight years old when he had begun to reign, and he reigned for thirty-one years in Jerusalem.
Yosiya yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara talatin da ɗaya.
2 And he did what was right in the sight of the Lord, and he walked in the ways of his father David. He did not turn away, neither to the right, nor to the left.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma yi tafiya a hanyoyin kakansa Dawuda, ba tare da juye dama ko hagu ba.
3 Now in the eighth year of his reign, when he was still a boy, he began to seek the God of his father David. And in the twelfth year after he had begun to reign, he cleansed Judah and Jerusalem from the high places, and the sacred groves, and the idols, and the graven images.
A shekara ta takwas ta mulkinsa, yayinda yake matashi, sai ya fara neman Allah na kakansa Dawuda. A shekara ta goma sha biyunsa ya fara tsabtacce Yahuda da Urushalima daga masujadan kan tudu, ginshiƙan Ashera, sassaƙaƙƙun gumaka da kuma siffofin da aka yi zubi.
4 And in his sight, they destroyed the altars of the Baals, and they demolished the idols which had been set upon them. And then he cut down the sacred groves and crushed the graven images. And he scattered the fragments upon the tombs of those who had been accustomed to immolate to them.
A ƙarƙashin umarninsa aka rurrushe bagadan Ba’al, ya kuma tumɓuke bagadan ƙona turare waɗanda suke a bisansu, ya farfashe ginshiƙan Ashera da kuma sassaƙaƙƙun siffofi. Ya ragargaza waɗannan kucu-kucu, ya barbaɗa su a kan kaburburan waɗanda suka miƙa musu hadayu.
5 And after that, he burned the bones of the priests upon the altars of the idols. And so did he cleanse Judah and Jerusalem.
Ya ƙone ƙasusuwan firistocin gumaka a kan bagaden da a dā suke miƙa hadayunsu, ta haka ya tsabtacce Yahuda da Urushalima.
6 Then too, in the cities of Manasseh, and of Ephraim, and of Simeon, even to Naphtali, he overturned everything.
Ya yi haka cikin garuruwan Manasse, Efraim da Simeyon, har zuwa Naftali, da kuma cikin kangwayen kewayensu,
7 And when he had destroyed the altars and the sacred groves, and had broken the idols to pieces, and when all the profane shrines had been demolished from the entire land of Israel, he returned to Jerusalem.
ya farfashe bagadai da ginshiƙan Ashera; ya niƙa gumaka suka zama gari, ya kuma yayyanka dukan bagadan turare kucu-kucu ko’ina a Isra’ila. Sa’an nan ya koma Urushalima.
8 And so, in the eighteenth year of his reign, having now cleansed the land and the temple of the Lord, he sent Shaphan, the son of Azaliah, and Maaseiah, the ruler of the city, and Joah, the son of Joahaz, the historian, to repair the house of the Lord his God.
A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya, ya tsarkake ƙasar da haikalin, ya aiki Shafan ɗan Azaliya da Ma’asehiya mai mulkin birni, tare da Yowa ɗan Yowahaz, marubuci, su gyara haikalin Ubangiji Allah.
9 And they went to Hilkiah, the high priest. And having accepted from him the money which had been brought into the house of the Lord, and which the Levites and porters had gathered together from Manasseh, and Ephraim, and the entire remnant of Israel, and also from all of Judah, and Benjamin, and the inhabitants of Jerusalem,
Suka tafi wurin Hilkiya babban firist suka ba shi kuɗin da aka kawo cikin haikalin Allah, wanda Lawiyawa masu tsaron ƙofofi sun tattara daga mutanen Manasse, Efraim da dukan raguwar Isra’ila da kuma daga dukan mutanen Yahuda da Benyamin da kuma mazaunan Urushalima.
10 they delivered it into the hands of those who were in charge of the workers in the house of the Lord, so that they might repair the temple, and restore whatever was weak.
Sa’an nan suka danƙa su ga mutanen da aka naɗa su lura da aiki a kan haikalin Ubangiji. Waɗannan mutane ne suke biyan ma’aikatan da suka gyara suka kuma mai da haikalin.
11 And they gave it to the artisans and the stoneworkers, so that they might buy stones from the quarries, and wood for the joints of the building and for the upper floors of the houses, which the kings of Judah had destroyed.
Suka kuma ba da kuɗi ga kafintoci da magina don su sayi sassaƙaƙƙun duwatsu, da katakai don yin tsaiko da tankar ginin da sarakunan Yahuda suka bari yă fāɗi ya zama kango.
12 And they did everything faithfully. Now the overseers of the workers were Jahath and Obadiah, from the sons of Merari, and Zechariah and Meshullam, from the sons of Kohath, who were supervising the work. All were Levites who knew how to play musical instruments.
Mutanen fa suka yi aiki da aminci. Shugabanninsu, su ne Yahat da Obadiya, Lawiyawa zuriyar Merari da Zakariya da Meshullam, zuriyar Kohat. Dukan Lawiyawa waɗanda suke gwanaye a kayan kiɗi,
13 Truly, scribes and teachers, from among the Levites who were porters, were over those who were carrying burdens for various uses.
sun lura da ma’aikata, suka kuma lura da dukan masu aiki daga aiki zuwa aiki. Waɗansu Lawiyawan su ne marubuta, magatakarda da kuma masu tsaron ƙofofi.
14 And when they carried out the money that had been brought into the temple of the Lord, Hilkiah the priest found the book of the law of the Lord by the hand of Moses.
Yayinda suke fitar da kuɗin da aka kai cikin haikalin Ubangiji, sai Hilkiya firist ya sami Littafin Dokar Ubangiji da aka bayar ta wurin Musa.
15 And he said to Shaphan, the scribe: “I have found the book of the law in the house of the Lord.” And he delivered it to him.
Hilkiya ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a cikin haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan.
16 Then he took the volume to the king, and he reported to him, saying: “Behold, everything that you entrusted to your servants is completed.
Sa’an nan Shafan ya ɗauki littafin zuwa wurin sarki, ya faɗa masa, “Manyan ma’aikatanka suna yin kome da aka sa su.
17 They have melted together the silver that was found in the house of the Lord. And it has been given to the overseers of the artisans and craftsmen for various works.
Mun ɗauke kuɗin da an ajiye a haikalin Ubangiji muka ba wa masu aiki da waɗanda suke lura da su.”
18 After this, Hilkiah the priest gave to me this book.” And when he had read it in the presence of the king,
Sa’an nan Shafan magatakarda ya sanar da sarki ya ce, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta daga cikinsa a gaban sarki.
19 and he had heard the words of the law, he tore his garments.
Da sarki ya ji kalmomin Doka, sai ya yage rigunansa.
20 And he instructed Hilkiah, and Ahikam, the son of Shaphan, and Abdon, the son of Micah, and also Shaphan, the scribe, and Asaiah, the servant of the king, saying:
Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya, Ahikam ɗan Shafan, Abdon ɗan Mika, Shafan magatakarda da kuma Asahiya mai hidimar sarki.
21 “Go, and pray to the Lord for me, and for the remnant of Israel and Judah, concerning all the words of this book, which has been found. For the great fury of the Lord has rained down upon us, because our fathers did not keep the words of the Lord, to do all that has been written in this volume.”
Ya ce, “Ku tafi ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da kuma saboda raguwa a Isra’ila da Yahuda game da abin da aka rubuta a wannan littafin da aka samu. Fushin Ubangiji mai girma ne da aka zuba a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye maganar Ubangiji ba; ba su aikata bisa ga dukan abin da yake a rubuce a wannan littafi ba.”
22 Therefore, Hilkiah, and those who had been sent with him by the king, went to Huldah, the prophetess, the wife of Shallum, the son of Tokhath, the son of Hasrah, the keeper of the vestments. She was living in Jerusalem, in the second part. And they spoke to her the words which we explained above.
Hilkiya tare da waɗanda sarki ya aika, suka tafi suka yi magana da annabiya Hulda, wadda take matar Shallum ɗan Tokhat ɗan Hasra, mai tsaron wurin ajiyar riguna. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
23 And she responded to them: “Thus says the Lord, the God of Israel: Tell the man who sent you to me:
Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce faɗa wa mutumin da ya aike ku gare ni,
24 Thus says the Lord: Behold, I will lead in evils over this place, and over its inhabitants, with all the curses that have been written in this book, which they have read before the king of Judah.
‘Ga abin da Ubangiji ya ce zai kawo masifa a wannan wuri da mutanensa, dukan la’anar da aka rubuta a cikin littafin da aka karanta a gaban sarkin Yahuda.
25 For they have abandoned me, and they have sacrificed to foreign gods, so that they provoked me to wrath by all the works of their hands. Therefore, my fury will rain down upon this place, and it will not be extinguished.
Domin sun yashe ni suka kuma ƙone turare wa waɗansu alloli, suka tsokane ni in yi fushi ta wurin dukan abin da hannuwansu suka yi, fushina zai zuba a kan wannan wuri, ba kuma za a kwantar da shi ba.’
26 To the king of Judah, who sent you to petition before the Lord, so shall you speak: Thus says the Lord, the God of Israel: Since you listened to the words of this volume,
Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yake cewa game da kalmomin da ka ji.
27 and your heart was softened, and you humbled yourself in the sight of God concerning these things which have been said against this place and against the inhabitants of Jerusalem, and since, revering my face, you have torn your garments, and have wept before me: I also have heeded you, says the Lord.
Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Allah sa’ad da ka ji abin da ya yi magana a kan wannan wuri da mutanensa, domin kuma ka ƙasƙantar da kanka a gabana, ka yage rigunanka ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
28 For now I will gather you to your fathers, and you will be brought into your sepulcher in peace. Neither shall your eyes see all the evil that I will lead in, over this place and over its inhabitants.” And so they took back to the king all that she had said.
Yanzu zan tara ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka ba za su ga dukan masifar da zan kawo a kan wannan wuri da kuma a kan waɗanda suke zama a nan ba.’” Sai suka kai amsar wa sarki.
29 And he, calling together all those greater by birth of Judah and Jerusalem,
Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
30 ascended to the house of the Lord, united with all the men of Judah, and the inhabitants of Jerusalem, the priests and the Levites, and all the people, from the least even to the greatest. And in their hearing, in the house of the Lord, the king read all the words of the volume.
Ya haura zuwa haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, mutanen Urushalima, firistoci da Lawiyawa, dukan mutane daga ƙarami zuwa babba. Ya karanta dukan kalmomin Littafin Alkawari wanda aka samu a cikin haikalin Ubangiji a kunnuwansu.
31 And standing up at his tribunal, he struck a covenant before the Lord, so that he would walk after him, and would keep his precepts and testimonies and justifications, with his whole heart and with his whole soul, and so that he would do the things that were written in that volume, which he had read.
Sai sarkin ya miƙe tsaye a inda yake, ya sabunta alkawari a gaban Ubangiji, don yă bi Ubangiji yă kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa da kuma farillansa da dukan zuciyarsa da kuma dukan ransa, ya kuma yi biyayya da kalmomin alkawarin da aka rubuta a cikin wannan littafi.
32 Also, concerning this, he bound by oath all who had been found in Jerusalem and Benjamin. And the inhabitants of Jerusalem acted in accord with the covenant of the Lord, the God of their fathers.
Sa’an nan ya sa kowa a Urushalima da Benyamin ya yi alkawari ga wannan; mutanen Urushalima suka aikata wannan bisa ga alkawarin Allah, Allah na kakanninsu.
33 Therefore, Josiah took away all the abominations from all the regions of the sons of Israel. And he caused all who were remaining in Israel to serve the Lord their God. During all his days, they did not withdraw from the Lord, the God of their fathers.
Yosiya ya fitar da dukan gumakan banƙyama daga dukan yankunan Isra’ilawa, ya kuma sa dukan waɗanda suke a Isra’ila su bauta wa Ubangiji Allahnsu. Muddin ransa, ba su fasa bin Ubangiji Allah na kakanninsu ba.

< 2 Chronicles 34 >