< 2 Chronicles 30 >

1 Also, Hezekiah sent to all of Israel and Judah. And he wrote letters to Ephraim and Manasseh, so that they would come to the house of the Lord in Jerusalem, and so that they would keep the Passover to the Lord, the God of Israel.
Sai Hezekiya ya aika wa dukan Isra’ila da Yahuda, ya kuma rubuta wasiƙu zuwa Efraim da Manasse, yana gayyatarsu su zo haikalin Ubangiji a Urushalima, su kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
2 Therefore, having taken counsel, the king and the rulers, and the entire assembly of Jerusalem, resolved that they would keep the Passover, in the second month.
Sarki da fadawansa da dukan taro a Urushalima suka yanke shawara su yi Bikin Ƙetarewa a wata na biyu.
3 For they had not been able to keep it at its proper time. For the priests, who were unable to suffice, had not been sanctified. And the people had not yet been gathered together in Jerusalem.
Ba su iya yinsa a daidai lokacinsa ba domin babu isashen firistocin da suka tsarkake kansu, mutane kuma ba su taru a Urushalima ba.
4 And the word was pleasing to the king, and to the entire multitude.
Shirin ya yi kyau ga sarki da kuma dukan taron.
5 And they resolved that they would send messengers to all of Israel, from Beersheba even to Dan, so that they might come and keep the Passover to the Lord, the God of Israel, at Jerusalem. For many had not kept it, just as it was prescribed by the law.
Suka yanke shawara su yi shelar a ko’ina a Isra’ila, daga Beyersheba zuwa Dan, suna kiran mutane su zo Urushalima, suka kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allah na Isra’ila. Ba a yi bikin da mutane masu yawa bisa ga abin da aka rubuta ba.
6 And carriers traveled with the letters, by order of the king and his rulers, to all of Israel and Judah, proclaiming, in accord with what the king had ordered: “O sons of Israel, return to the Lord, the God of Abraham, and Isaac, and Israel. And he will return to the remnant who escaped from the hand of the king of the Assyrians.
Bisa ga umarnin sarki, sai’yan aika suka tafi ko’ina a Isra’ila da Yahuda da wasiƙu daga sarki da kuma daga fadawansa, wasiƙar tana cewa, “Mutanen Isra’ila, ku dawo ga Ubangiji Allah na Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, domin yă dawo gare ku, ku da kuka tafi, ku da kuka kuɓuce daga hannun sarakuna Assuriya.
7 Do not choose to be like your fathers and brothers, who withdrew from the Lord, the God of their fathers. And so he delivered them over to destruction, as you yourselves discern.
Kada ku zama kamar iyayenku da’yan’uwanku, waɗanda suka yi rashin aminci ga Ubangiji Allah na kakanninsu, har ya mai da su abin tsoro, yadda kuke gani.
8 Do not choose to harden your necks, as your fathers did. Surrender to the hands of the Lord. And go to his Sanctuary, which he has sanctified unto eternity. Serve the Lord, the God of your fathers, and the fury of his wrath will be turned away from you.
Kada ku yi taurinkai, yadda iyayenku suka yi; ku miƙa kai ga Ubangiji. Ku zo wuri mai tsarki, wanda ya tsarkake har abada. Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, domin fushi mai zafi yă juye daga gare ku.
9 For if you will return to the Lord, your brothers and sons will find mercy before their masters, who led them away as captives, and they will be returned to this land. For the Lord your God is compassionate and lenient, and he will not avert his face from you, if you will return to him.”
In kuka dawo wurin Ubangiji, sa’an nan waɗanda suka kama’yan’uwanku da’ya’yanku za su nuna musu tausayi, su kuma dawo wannan ƙasa, gama Ubangiji Allahnku mai alheri ne mai jinƙai kuma. Ba zai kau da fuskarsa daga gare ku ba, in kuka dawo gare shi.”
10 And so, the carriers were traveling quickly from city to city, throughout the land of Ephraim and Manasseh, as far as Zebulun, though they were ridiculing and mocking them.
’Yan aika suka tafi gari-gari a cikin Efraim da Manasse, har zuwa Zebulun, amma mutane suka yi musu dariyar reni, suka kuma yi musu ba’a.
11 Even so, certain men from Asher, and from Manasseh, and from Zebulun, acquiescing to this counsel, went to Jerusalem.
Duk da haka, waɗansu mutanen Asher, Manasse da Zebulun suka ƙasƙantar da kansu suka tafi Urushalima.
12 Truly, the hand of God was working in Judah, to give them one heart, so that they would accomplish the word of the Lord, according to the precept of the king and of the rulers.
Haka ma a Yahuda, hannun Allah yana a kan mutane don yă ba su zuciya ɗaya su yi abin da sarki da fadawansa suka umarta, suna bin maganar Ubangiji.
13 And many people gathered together in Jerusalem, so that they could keep the solemnity of unleavened bread, in the second month.
Taron mutane mai girma ya haɗu a Urushalima don Bikin Burodi Marar Yisti a wata na biyu.
14 And rising up, they destroyed the altars which were in Jerusalem, and all the things in which incense was burned to idols. Overturning these things, they cast them into the torrent Kidron.
Suka kawar da bagadai a Urushalima suka fid da bagadan turare suka zubar da su a Kwarin Kidron.
15 Then they immolated the Passover on the fourteenth day of the second month. Also, the priests and Levites, at length having been sanctified, offered the holocausts in the house of the Lord.
Suka yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a rana ta goma sha huɗu na wata na biyu. Firistoci da Lawiyawa suka ji kunya suka tsarkake kansu, suka kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
16 And they stood in their order, according to the disposition and law of Moses, the man of God. Yet truly, the priests took up the blood, which was to be poured out, from the hands of the Levites,
Sa’an nan suka ɗauki matsayinsu na kullum yadda yake a Dokar Musa mutumin Allah. Firistoci suka yayyafa jinin da Lawiyawa suka ba su.
17 because a great number were not sanctified. And therefore, the Levites immolated the Passover for those who had not been sanctified to the Lord in time.
Da yake da yawa cikin taron ba su tsarkake kansu ba, dole Lawiyawa su yanka’yan ragunan Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda ba su da tsarki, ba su kuma iya tsarkake ragunansu ga Ubangiji ba.
18 And now a great portion of the people from Ephraim, and Manasseh, and Issachar, and Zebulun, who had not been sanctified, ate the Passover, which is not in accord with what was written. And Hezekiah prayed for them, saying: “The good Lord will be forgiving
Ko da yake yawancin mutanen da suka zo daga Efraim, Manasse, Issakar da Zebulun ba su tsarkake kansu ba, duk da haka suka ci Bikin Ƙetarewa, ba tare da bin abin da yake a rubuce ba. Amma Hezekiya ya yi addu’a dominsu cewa, “Bari Ubangiji, wanda yake nagari, yă gafarta wa kowa
19 to all who, with their whole heart, seek the Lord, the God of their fathers. And he will not impute it to them, though they have not been sanctified.”
wanda ya sa zuciyarsa ga neman Allah, Ubangiji Allah na kakanninsa, ko da shi marar tsarki ne bisa ga dokokin wuri mai tsarki.”
20 And the Lord heeded him, and was reconciled to the people.
Ubangiji kuwa ya ji Hezekiya ya kuma warkar da mutane.
21 And the sons of Israel who were found at Jerusalem kept the solemnity of unleavened bread for seven days with great rejoicing, praising the Lord throughout each day, with the Levites and the priests, accompanied by the musical instruments corresponding to their office.
Isra’ilawan da suka kasance a Urushalima suka yi Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai da farin ciki mai girma, yayinda Lawiyawa da firistoci suke rera ga Ubangiji kowace rana, haɗe da kayan kiɗin yabon Ubangiji.
22 And Hezekiah spoke to the heart of all the Levites, who had a good understanding concerning the Lord. And they ate during the seven days of the solemnity, immolating victims of peace offerings, and praising the Lord, the God of their fathers.
Hezekiya ya yi magana mai ƙarfafawa ga dukan Lawiyawa waɗanda suka nuna ganewar fasaha a hidimar Ubangiji. Kwana bakwai suka ci rabonsu da aka tsara, suka miƙa hadayun salama, suka kuma yabi Ubangiji Allah na kakanninsu.
23 And it pleased the entire multitude that they should celebrate, even for another seven days. And they did this with enormous gladness.
Dukan mutanen suka yarda su ƙara kwana bakwai kuma, sai suka ci gaba da bikin cikin farin ciki har waɗansu kwana bakwai kuma.
24 For Hezekiah, the king of Judah, had offered to the multitude one thousand bulls and seven thousand sheep. Truly, the rulers had given the people one thousand bulls and ten thousand sheep. Then a great multitude of priests was sanctified.
Hezekiya sarkin Yahuda ya tanada bijimai dubu ɗaya da tumaki da kuma awaki dubu bakwai wa taron, fadawa kuma suka tanada musu bijimai dubu da kuma tumaki da awaki dubu goma. Firistoci masu yawa suka tsarkake kansu.
25 And the whole multitude of Judah, as much the priests and Levites as the entire crowd that had arrived from Israel, and also the converts from the land of Israel, and those with a habitation in Judah, was overflowing with cheerfulness.
Taron gaba ɗaya na Yahuda suka yi farin ciki, tare da firistoci da kuma Lawiyawa da dukan waɗanda suka taru daga Isra’ila, har ma da baƙi waɗanda suka zo daga Isra’ila da waɗanda suke zama a Yahuda.
26 And there was a great celebration in Jerusalem, to such an extent as had not been in that city since the days of Solomon, the son of David, the king of Israel.
Aka yi farin ciki mai girma a Urushalima, gama tun zamanin Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila, ba a taɓa yin wani abu kamar haka a Urushalima ba.
27 Then the priests and Levites rose up and blessed the people. And their voice was heeded. And their prayer reached the holy habitation of heaven.
Firistoci da Lawiyawa suka tsaya suka albarkace mutane, Allah kuma ya ji su, gama addu’arsu ya kai sama, mazauninsa mai tsarki.

< 2 Chronicles 30 >