< 2 Chronicles 26 >

1 Then all the people of Judah appointed his son, Uzziah, who was sixteen years old, as king in place of his father, Amaziah.
Sai dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Uzziya wanda yake da shekara goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
2 He built up Eloth, and he restored it to the dominion of Judah. After this, the king slept with his fathers.
Shi ne wanda ya sāke gina Elot ya kuma mai da shi ga Yahuda bayan Amaziya ya huta tare da kakanninsa.
3 Uzziah was sixteen years old when he had begun to reign. And he reigned for fifty-two years in Jerusalem. The name of his mother was Jecoliah, from Jerusalem.
Uzziya yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya ce; ita daga Urushalima ce.
4 And he did what was right in the eyes of the Lord, in accord with all that his father, Amaziah, had done.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
5 And he sought the Lord, during the days of Zechariah, who understood and saw God. And while he was seeking the Lord, he directed him in all things.
Ya nemi Allah a kwanakin Zakariya, wanda ya koyar da shi a tsoron Allah. Muddin ya nemi Ubangiji, Allah ya ba shi nasara.
6 Indeed, he went out and fought against the Philistines. And he destroyed the wall of Gath, and the wall of Jabneh, and the wall of Ashdod. Also, he built towns in Ashdod, and among the Philistines.
Ya yi yaƙi da Filistiyawa ya kuma rushe katangar Gat, Yabne da kuma Ashdod. Sa’an nan ya sāke gina garuruwa kusa da Ashdod da sauran wurare a cikin Filistiyawa.
7 And God helped him against the Philistines, and against the Arabians, who were living in Gurbaal, and against the Ammonites.
Allah ya taimake shi a kan Filistiyawa da kuma a kan Larabawa waɗanda suke zama a Gur-Ba’al da kuma a kan Meyunawa.
8 And the Ammonites weighed out gifts to Uzziah. And his name became widely known, even to the entrance of Egypt, because of his frequent victories.
Ammonawa suka kawo haraji wa Uzziya, sunan da ya yi kuwa ya bazu har iyakar Masar, domin ya zama mai iko sosai.
9 And Uzziah built towers in Jerusalem, above the gate of the corner, and above the gate of the valley, and others on the same side of the wall, and he fortified them.
Uzziya ya gina hasumiyoyi a Urushalima a Ƙofar Kusurwa, a Ƙofar Kwari da kuma a kusurwar katanga, ya kuma yi musu katanga.
10 Then he also constructed towers in the wilderness, and dug many cisterns, because he had much cattle, both in the plains and in the starkness of the wilderness. Also, he had vineyards and dressers of vines in the mountains and at Carmel. Certainly, he was a man devoted to agriculture.
Ya gina hasumiyoyi a hamada ya kuma haƙa rijiyoyi masu yawa, gama yana da dabbobi masu yawa a gindin duwatsu da kuma a kwari. Yana da mutane masu yin masa aiki a gonakinsa da gonakin inabinsa a tuddai da kuma a ƙasashe masu dausayi, gama yana son noma.
11 Now the army of his warriors, who would go forth to battle, was under the hand of Jeiel, the scribe, and Maaseiah, the teacher, and under the hand of Hananiah, who was among the king’s commanders.
Uzziya ya kasance da gogaggun mayaƙa, a shirye su fito ɓangarori-ɓangarori bisa ga yawansu yadda Yehiyel magatakarda, da Ma’asehiya jarumi, suka karkasa su bisa ga umarnin Hananiya, ɗaya daga cikin fadawa.
12 And the entire number of the leaders, by the families of strong men, was two thousand six hundred.
Yawan shugabannin iyali a bisa jarumawa sun kai 2,600.
13 And the entire army under them was three hundred and seven thousand five hundred, who were fit for war, and who fought on behalf of the king against the adversaries.
A ƙarƙashin shugabancinsu akwai mayaƙa 307,500 horarru don yaƙi, mayaƙa masu ƙarfi don su taimaki sarki a kan abokan gābansa.
14 Also, Uzziah prepared for them, that is, for the entire army, shields, and spears, and helmets, and breastplates, and bows, as well as slings for the casting of stones.
Uzziya ya tanada garkuwoyi, māsu, hulunan kwano, kayan sulke, baka da majajjawa don mayaƙan gaba ɗaya.
15 And in Jerusalem, he made various kinds of machines, which he placed in the towers, and at the corners of the walls, so as to shoot arrows and large stones. And his name went forth to far away places, for the Lord was helping him and had strengthened him.
A Urushalima ya yi na’urori da gwanaye suka sarrafa don amfani a hasumiyoyi da kuma a kusurwar kāriya don harbin kibiyoyi da jefan manyan duwatsu. Sunansa ya bazu ko’ina, gama ya sami taimako sosai har ya zama mai iko.
16 But when he had become strong, his heart was lifted up, even to his own destruction. And he neglected the Lord his God. And entering into the temple of the Lord, he intended to burn incense upon the altar of incense.
Amma bayan Uzziya ya zama mai iko, sai ɗaga kai ya kai shi ga fāɗuwa. Bai yi aminci ga Ubangiji Allahnsa ba, ya kuma shiga haikalin Ubangiji don yă ƙone turare a bagaden turare.
17 And entering immediately after him, Azariah the priest, and with him eighty priests of the Lord, very valiant men,
Azariya firist tare da waɗansu firistoci tamanin na Ubangiji masu ƙarfin hali suka bi shi ciki.
18 withstood the king, and they said: “It is not your office, Uzziah, to burn incense to the Lord; rather, it is the office of the priests, that is, of the sons of Aaron, who have been consecrated for this same ministry. Depart from the sanctuary, otherwise you will be in contempt. For this act will not be reputed to you for your glory by the Lord God.”
Suka kalubalance shi suka ce, “Ba daidai ba ne, Uzziya, ka ƙone turare ga Ubangiji. Wannan aikin firistoci zuriyar Haruna ne, waɗanda aka tsarkake don ƙone turare. Ka bar wuri mai tsarki, gama ka kasance marar aminci; kuma Ubangiji Allah ba zai girmama ka ba.”
19 And Uzziah, having become angry, while holding in his hand the censer so that he might burn incense, threatened the priests. And immediately a leprosy arose on his forehead, in the sight of the priests, in the house of the Lord, at the altar of incense.
Uzziya wanda yake da farantin wuta a hannunsa a shirye don ƙone turare, ya husata. Yayinda yake fushi da firistocin a gabansu a gaban bagaden turare a haikalin Ubangiji, sai kuturta ta faso a goshinsa.
20 And when the high priest Azariah, and all the rest of the priests, had gazed upon him, they saw the leprosy on his forehead, and they hurried to expel him. Then too, he himself, becoming terrified, rushed to depart, because immediately he had become aware of the wound of the Lord.
Sa’ad da Azariya babban firist da dukan sauran firistoci suka dube shi, sai suka ga cewa yana da kuturta a goshinsa, saboda haka suka gaggauta tunkuɗa shi waje nan da nan. Tabbatacce, shi kansa ma ya yi marmari yă bar wurin domin Ubangiji ya buge shi.
21 And so, king Uzziah was a leper, even until the day of his death. And he lived in a separate house, being full of leprosy, because of which he had been ejected from the house of the Lord. Then Jotham, his son, directed the house of the king, and he was judging the people of the land.
Sarki Uzziya ya kasance da kuturta har ranar mutuwarsa. Ya zauna a gidan da aka ware, da kuturci, aka kuma ware shi daga haikalin Ubangiji. Yotam ɗansa ya lura da fadan ya kuma yi mulkin mutanen ƙasar.
22 But the rest of the words of Uzziah, the first and the last, were written by the prophet Isaiah, the son of Amoz.
Sauran ayyukan mulkin Uzziya daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce ta hannun annabi Ishaya ɗan Amoz.
23 And Uzziah slept with his fathers. And they buried him in the field of the royal sepulchers, because he was a leper. And Jotham, his son, reigned in his place.
Uzziya ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi kusa da su a fili don binnewar da take ta sarakuna, domin mutane sun ce, “Yana da kuturta.” Sai Yotam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 2 Chronicles 26 >