< 2 Chronicles 22 >

1 Then the inhabitants of Jerusalem appointed his youngest son, Ahaziah, as king in his place. For the robbers of the Arabians, who had fallen upon the camp, had put to death all those who were greater by birth before him. And so Ahaziah, the son of Jehoram, reigned as king of Judah.
Mutanen Urushalima suka mai da Ahaziya, autan Yehoram, sarki a madadinsa, da yake’yan hari, waɗanda suka zo tare da Larabawa cikin sansani, sun kashe dukan manyan’ya’yansa. Saboda haka Ahaziya ɗan Yeroham sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Ahaziah was forty-two years old when he had begun to reign, and he reigned for one year in Jerusalem. And the name of his mother was Athaliah, the daughter of Omri.
Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara guda. Sunan mahaifiyarsa Ataliya ce, jikanyar Omri.
3 But he too went forth in the ways of the house of Ahab. For his mother impelled him to act impiously.
Shi ma ya yi tafiya a hanyoyin gidan Ahab, gama mahaifiyarsa ta ƙarfafa shi yă yi abin da ba shi da kyau.
4 And so he did evil in the sight of the Lord, just as the house of Ahab did. For after the death of his father, they were counselors to him, to his destruction.
Ya aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, yadda gidan Ahab ta yi, gama bayan mutuwar mahaifinsa, sai gidan Ahab ta zama masu ba shi shawara, shawarar da ta kai shi ga lalacewa.
5 And he walked in their counsels. And he went with Joram, the son of Ahab, the king of Israel, to war against Hazael, the king of Syria, at Ramoth Gilead. And the Syrians wounded Joram.
Ya kuma bi shawararsu sa’ad da ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab sarkin Isra’ila don yă yaƙi Hazayel sarkin Aram a Ramot Gileyad. Sai Arameyawa suka yi wa Yoram rauni;
6 And he returned, so that he might be cured at Jezreel. For he had received many wounds in the above-stated battle. And so Ahaziah, the son of Jehoram, the king of Judah, descended, so that he might visit Joram, the son of Ahab, at Jezreel, while he was ill.
saboda haka ya dawo Yezireyel don yă yi jinyar raunin da suka yi masa a Rama cikin yaƙinsa da Hazayel sarkin Aram. Sa’an nan Azariya ɗan Yehoram sarkin Yahuda ya gangara zuwa Yezireyel don yă ga Yoram ɗan Ahab domin ya ji rauni.
7 Indeed, it was the will of God against Ahaziah that he would go to Joram, and when he had gone, that he also would go out with him against Jehu, the son of Nimshi, whom the Lord had anointed to destroy the house of Ahab.
Ta wurin ziyarar Yoram, Allah ya kawo fāɗuwar Ahaziya. Sa’ad da Ahaziya ya iso, ya tafi tare da Yoram domin yă sadu da Yehu ɗan Nimshi, wanda Ubangiji ya shafe don yă hallaka gidan Ahab.
8 Therefore, when Jehu was overthrowing the house of Ahab, he found the leaders of Judah, with the sons of the brothers of Ahaziah, who were ministering to him, and he put them to death.
Yayinda Yehu yake hukunta wa gidan Ahab, sai ya sami fadawan Yahuda da kuma’ya’yan dangin Ahaziya maza, waɗanda suke yi wa Ahaziya hidima, sai ya kashe su.
9 Also, while he himself was seeking Ahaziah, he found him to be hiding in Samaria. And having been led to him, he killed him. And they buried him, because he was the son of Jehoshaphat, who had sought the Lord with all his heart. But there was no longer any hope that someone from the stock of Ahaziah would reign.
Ya kuma sa aka nemi Ahaziya. Aka kamo shi sa’ad da ya ɓuya a Samariya, suka kawo shi wurin Yehu, suka kashe shi, suka binne shi, gama sun ce, “Shi jikan Yehoshafat ne, wanda ya nemi Ubangiji da dukan zuciyarsa.” Ta haka babu wani a gidan Ahaziya da yake da ƙarfin cin gaba da mulkin.
10 For indeed, his mother, Athaliah, seeing that her son had died, rose up and killed the entire royal stock of the house of Jehoram.
Sa’ad da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga cewa ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta hallaka dukan’yan gidan sarautar Yahuda.
11 But Jehosheba, the daughter of the king, took Joash, the son of Ahaziah, and stole him from the midst the king’s sons when they were being slain. And she hid him with his nurse in a bedroom. Now Jehosheba, the one who had hidden him, was the daughter of king Jehoram, and the wife of the high priest Jehoiada, and the sister of Ahaziah. And because of this, Athaliah did not kill him.
Amma Yehosheba,’yar Sarki Yehoram, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya ta sace shi daga cikin’ya’yan gidan sarauta waɗanda ake shiri a kashe, ta sa shi tare da mai renonsa a ɗakin kwana. Haka fa, Yehosheba’yar sarki Yoram, matar Yehohiyada firist, ta yi, gama ita’yar’uwar Ahaziya ce, ta ɓoye Yowash don kada Ataliya tă kashe shi.
12 Therefore, he was with them, hidden in the house of God, for six years, while Athaliah reigned over the land.
Ya kasance a ɓoye tare da su a haikalin Allah shekara shida, yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.

< 2 Chronicles 22 >