< 2 Chronicles 19 >

1 Then Jehoshaphat, the king of Judah, returned in peace to his house in Jerusalem.
Sa’ad da Yehoshafat sarkin Yahuda ya dawo zuwa fadansa a Urushalima lafiya,
2 And the seer Jehu, the son of Hanani, met him, and said to him: “You offer assistance to the impious, and you are joined in friendship with those who hate the Lord. And for this reason, you certainly deserve the wrath of the Lord.
Yehu mai duba, ɗan Hanani, ya fita don yă tarye shi, ya kuma ce wa sarki, “Ya yi kyau ke nan da ka taimaki mugu ka kuma ƙaunaci waɗanda suke ƙin Ubangiji? Da yake ka yi haka fushin Ubangiji yana a kanka
3 But good works have been found in you. For you have taken away the sacred groves from the land of Judah. And you have prepared your heart, so as to seek the Lord, the God of your fathers.”
Duk da haka an sami wani abin kirki a wurinka, gama ka kawar da ginshiƙan Ashera a ƙasar, ka kuma sa zuciyarka a kan neman Allah.”
4 Then Jehoshaphat lived in Jerusalem. And again he went out to the people, from Beersheba as far as mount Ephraim. And he called them back to the Lord, the God of their fathers.
Yehoshafat ya zauna a Urushalima, ya kuma fita yana shiga cikin mutane daga Beyersheba zuwa ƙasar tudun Efraim ya kuma juyar da su ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
5 And he appointed judges of the land, in all the fortified cities of Judah, in each place.
Ya naɗa alƙalai a kowanne daga cikin biranen katanga na Yahuda a ƙasar.
6 And instructing the judges, he said: “Pay attention to what you are doing. For you exercise judgment, not of man, but of the Lord. And whatever you will have judged, it will come back to you.
Ya faɗa musu, “Ku lura da abin da kuke yi, gama shari’ar da kuke yi ba ta mutum ba ce, amma ta Ubangiji ce, yana tare da ku sa’ad da kuke yanke shari’a.
7 Let the fear of the Lord be with you, and do all things with diligence. For there is no iniquity with the Lord our God, nor respect of persons, nor desire for gifts.”
Yanzu fa ku ji tsoron Ubangiji. Ku yi hankali a kan abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu ba ya sonkai ko nuna wariya ko cin hanci.”
8 Jehoshaphat also appointed Levites and priests and leaders of families, out of Israel, in Jerusalem, so that they might judge the judgment and purpose of the Lord for its inhabitants.
A Urushalima kuma, Yehoshafat ya naɗa waɗansu Lawiyawa, firistoci da kawunan iyalan Isra’ilawa don su tabbatar da an bi dokar Ubangiji, su kuma sasanta tsakanin mutane. A Urushalima za su zauna.
9 And he instructed them, saying, “So shall you act: faithfully, in the fear of the Lord, and with a perfect heart.
Ya ba su waɗannan umarnai, “Ku yi aikinku da aminci da tsoron Ubangiji da dukan zuciyarku.
10 Every case that will come to you from your brothers, who live in their cities, between kindred and kindred, wherever there is a question concerning law, commandment, ceremonies, or justifications, reveal it to them, so that they may not sin against the Lord, and so that wrath may not overwhelm you and your brothers. Then, by acting in this way, you will not sin.
Cikin kowane batun da ya zo gabanku daga’yan’uwanku waɗanda suke zama a birane, ko batun na kisa ne ko kuwa waɗansu batuttuwan da suka shafi doka, umarnai, ƙa’idodi ko farillai, dole ku ja musu kunne kada su yi wa Ubangiji zunubi; in ba haka ba fushinsa zai sauko a kanku da’yan’uwanku. Ku yi wannan, ta haka ba za ku kuwa yi zunubi ba.
11 But Amariah, a priest and your high priest, shall preside over those things which pertain to God. Then Zebadiah, the son of Ishmael, who is a ruler in the house of Judah, shall be over those works that pertain to the office of the king. And you have before you the Levites as teachers. Be strengthened and act diligently, and the Lord will be with you for what is good.”
“Amariya, babban firist, shi ne zai shugabance ku a kan dukan al’amuran da suke na wajen Ubangiji, Zebadiya ɗan Ishmayel kuwa, shugabanku a kan dukan al’amuran da suka shafi sarki, Lawiyawa kuma za su zama a matsayin manya a gabanku. Ku yi abubuwa da ƙarfin hali, bari kuma Ubangiji yă kasance tare da masu yin gaskiya.”

< 2 Chronicles 19 >