< 2 Chronicles 11 >

1 Then Rehoboam went to Jerusalem, and he called together the entire house of Judah and of Benjamin, one hundred eighty thousand elect men of war, so that he might contend against Israel, and turn back his kingdom to himself.
Sa’ad da Rehobowam ya iso Urushalima, ya tattara mayaƙa dubu ɗari takwas daga gidan Yahuda da Benyamin, don su yi yaƙi da Isra’ila su sāke mai da mulki wa Rehobowam.
2 And the word of the Lord came to Shemaiah, the man of God, saying:
Amma wannan maganar Ubangiji ta zo ga Shemahiya mutumin Allah.
3 “Speak to Rehoboam, the son of Solomon, the king of Judah, and to all of Israel who are of Judah, or of Benjamin:
“Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon sarkin Yahuda da kuma dukan Isra’ilawan da suke a Yahuda da Benyamin,
4 Thus says the Lord: You shall not ascend and fight against your brothers. Let each one return to his own house. For it is by my will that this has happened.” And when they had heard the word of the Lord, they turned back, and they did not continue on against Jeroboam.
‘Ga abin da Ubangiji ya ce kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku. Ku tafi gida kowannenku, gama wannan yi na ne.’” Saboda haka suka yi biyayya ga maganar Ubangiji suka kuma koma daga takawa don yaƙi da Yerobowam.
5 Then Rehoboam lived in Jerusalem, and he built fortified cities in Judah.
Rehobowam ya zauna a Urushalima ya kuma gina garuruwa don kāriya a cikin Yahuda.
6 And he built up Bethlehem, and Etam, and Tekoa,
Betlehem, Etam, Tekowa,
7 and also Bethzur, and Soco, and Adullam,
Bet-Zur, Soko, Adullam,
8 indeed also Gath, and Mareshah, and Ziph,
Gat, Maresha, Zif,
9 then too Adoram, and Lachish, and Azekah,
Adorayim, Lakish, Azeka,
10 as well as Zorah, and Aijalon, and Hebron, which were very fortified cities in Judah and in Benjamin.
Zora, Aiyalon da Hebron. Waɗannan su ne garuruwan katanga a cikin Yahuda da Benyamin.
11 And when he had enclosed them with walls, he placed in them rulers, and storehouses of provisions, that is, of oil and wine.
Ya ƙarfafa kāriyarsu ya kuma sa shugabannin mayaƙa a cikinsu, tare da tanadin abinci, man zaitun da kuma ruwan inabi.
12 Moreover, in each city he made an armory of shields and spears, and he strengthened them with the utmost diligence. And he ruled over Judah and Benjamin.
Ya sa garkuwoyi da māsu a cikin dukan biranen, ya kuma sa suka zama da ƙarfi. Saboda haka Yahuda da Benyamin suka zama nasa.
13 Then the priests and Levites, who were in all of Israel, came to him from all their settlements,
Firistoci da Lawiyawa daga dukan yankuna ko’ina a Isra’ila suka haɗa kai da shi.
14 leaving behind their suburbs and possessions, and crossing over to Judah and to Jerusalem. For Jeroboam and his followers had cast them out, so that they could not exercise the priestly office to the Lord.
Lawiyawa suka ma bar makiyayansu da mallakarsu, suka zo Yahuda da Urushalima domin Yerobowam da’ya’yansa maza sun ƙi su a matsayin firistocin Ubangiji.
15 And he appointed for himself priests of high places, and of demons, and of calves that he had made.
Yerobowam ya naɗa firistocinsa domin masujadan kan tudu da kuma domin gumakan nan na akuya da maraƙin da ya yi.
16 Moreover, out of all the tribes of Israel, whosoever would give their heart so that they sought the Lord God of Israel, they went to Jerusalem to immolate their victims before the Lord, the God of their fathers.
Waɗanda suke daga kowane kabilar Isra’ila waɗanda suka sa zuciya a kan neman Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka bi Lawiyawa zuwa Urushalima don su miƙa hadayu ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
17 And they strengthened the kingdom of Judah, and they confirmed Rehoboam, the son of Solomon, for three years. For they walked in the ways of David and of Solomon, but only for three years.
Suka ƙarfafa mulkin Yahuda suka kuma goyi bayan Rehobowam ɗan Solomon shekaru uku, suna tafiya a hanyoyin Dawuda da Solomon a wannan lokaci.
18 Then Rehoboam took as wife Mahalath, the daughter of Jerimoth, son of David, and also Abihail, the daughter of Eliab, son of Jesse.
Rehobowam ya auri Mahalat,’yar Yerimot ɗan Dawuda wadda Abihayil’yar Eliyab ɗan Yesse ta haifa.
19 They bore sons for him: Jeush, and Shemariah, and Zaham.
Ta haifa masa’ya’ya maza. Yewush, Shemariya da Zaham.
20 And also after her, he married Maacah, the daughter of Absalom, who bore for him Abijah, and Attai, and Ziza, and Shelomith.
Sa’an nan ya auri Ma’aka’yar Absalom, wadda ta haifa masa Abiya, Attai, Ziza da kuma Shelomit.
21 But Rehoboam loved Maacah, the daughter of Absalom, above all his wives and concubines. For he had taken eighteen wives and sixty concubines. And he conceived twenty-eight sons and sixty daughters.
Rehobowam ya ƙaunaci Ma’aka’yar Absalom fiye da sauran matansa da ƙwarƙwaransa. Duka-duka dai ya auri mata goma sha takwas da ƙwarƙwarai sittin, yana da’ya’ya maza ashirin da takwas da’ya’ya mata sittin.
22 Truly, he appointed as the head, Abijah, the son of Maacah, to be the ruler over all his brothers. For he thought to make him king,
Rehobowam ya naɗa Abiya ɗan Ma’aka yă zama babba yerima a cikin’yan’uwansa, don dai yă naɗa shi sarki.
23 since he was wiser and more powerful than all his sons, even in all the regions of Judah and Benjamin, and in all the fortified cities. And he provided them with very much food, and he sought many wives.
Ya yi hikima, ya watsar da waɗansu’ya’yansa a dukan yankunan Yahuda da Benyamin, da kuma a dukan birane masu katanga. Ya ba su tanadi mai yawa ya kuma aurar musu mata masu yawa.

< 2 Chronicles 11 >