< 1 Samuel 26 >

1 And the Ziphites went to Saul at Gibeah, saying: “Behold, David is hidden on the hill of Hachilah, which is opposite the wilderness.”
Zifawa suka je wurin Shawulu a Gibeya suka ce, “Ashe, ba Dawuda ne ya ɓuya a tudun Hakila da yake fuskantar Yeshimon ba?”
2 And Saul rose up, and he descended into the desert of Ziph, and with him three thousand elect men of Israel, so that he might seek David in the desert of Ziph.
Sai Shawulu ya tashi ya gangara zuwa Jejin Zif, tare da zaɓaɓɓun mutane dubu uku na Isra’ila. Suka fita neman Dawuda a can.
3 And Saul encamped at Gibeah on Hachilah, which was opposite the wilderness on the way. But David was living in the desert. Then, seeing that Saul had arrived after him in the wilderness,
Shawulu ya yi sansani a bakin hanyar zuwa tudun Hakila mai fuskantar Yeshimon. Amma Dawuda yana zaune a jeji. Sa’ad da ya ga Shawulu ya biyo shi har zuwa can,
4 he sent explorers, and he learned that he certainly had arrived in that place.
sai ya aiki’yan leƙen asiri su tabbata lalle Shawulu ya iso can.
5 And David rose up secretly, and he went to the place where Saul was. And when he had seen the place where Saul was sleeping, and Abner, the son of Ner, the leader of his military, and Saul sleeping in a tent, and the remainder of the common people all around him,
Sai Dawuda ya kintsa ya tafi inda Shawulu ya yi sansani. Ya ga inda Shawulu da Abner ɗan Ner shugaban ƙungiyar soja suka kwanta. Shawulu yana kwance a cikin sansani tare da sojoji kewaye da shi.
6 David spoke to Ahimelech, the Hittite, and to Abishai, the son of Zeruiah, the brother of Joab, saying, “Who will descend with me to Saul in the camp?” And Abishai said, “I will descend with you.”
Sai Dawuda ya ce wa Ahimelek mutumin Hitti da Abishai ɗan Zeruhiya ɗan’uwan Yowab, “Wa zai gangara tare da ni zuwa sansanin Shawulu?” Sai Abishai ya ce, “Zan tafi tare da kai.”
7 Therefore, David and Abishai went to the people by night, and they found Saul lying down and sleeping in the tent, with his spear fixed in the ground at his head. And Abner and the people were sleeping all around him.
Saboda haka Dawuda da Abishai suka gangara zuwa wurin rundunar da dare, sai ga Shawulu kwance yana barci a cikin sansani da māshinsa a kafe a ƙasa kusa da kansa. Abner kuwa tare da sojoji suna kwance kewaye da shi.
8 And Abishai said to David: “God has enclosed your enemy this day in your hands. Now therefore, I will pierce him with my lance, through to the ground, once, and there will not need to be a second.”
Abishai ya ce wa Dawuda, “Yau Allah ya ba da maƙiyinka a hannunka. Bari in kafe shi da ƙasa da māshina, zan soke shi da māshi sau ɗaya tak, ba na bukata in soke shi sau biyu.”
9 And David said to Abishai: “You shall not kill him. For who may extend his hand against the Christ of the Lord, and yet be innocent?”
Amma Dawuda ya ce wa Abishai, “Kada ka hallaka shi. Wa zai sa hannu a kan shafaffe na Ubangiji, har yă tsira?
10 And David said: “As the Lord lives, unless the Lord himself will strike him, or unless his day to die will have arrived, or unless, descending into battle, he will perish,
Muddin Ubangiji yana a raye, Ubangiji da kansa zai buge shi, ko yă mutu a lokacinsa, ko kuma yă mutu a wurin yaƙi.
11 may the Lord be gracious to me, so that I may not extend my hand against the Christ of the Lord. Now therefore, take the spear that is at his head, and the cup of water, and let us go.”
Amma Allah yă sawwaƙa in sa hannu a shafaffen Ubangiji, ka ɗauki māshin da butar ruwan da take kusa da kansa mu tafi.”
12 And so, David took the spear, and the cup of water that was at Saul’s head, and they went away. And there was no one who saw it, or realized it, or awakened, but they were all sleeping. For a deep sleep from the Lord had fallen over them.
Saboda haka Dawuda ya ɗauki māshin da butar ruwan da take kusa da Shawulu suka tafi. Ba wanda ya gan su, ba wanda ya san abin da ya faru, ba kuwa wanda ya farka, dukansu suna barci gama Ubangiji ya sa barci mai nauyi ya ɗauke su.
13 And when David had crossed over to the opposite side, and had stood upon the top of the hill far away, so that there was a great interval between them,
Sa’an nan Dawuda ya haye zuwa wancan gefen kwarin, ya hau kan wani tudu mai ɗan nisa inda Shawulu tare da mutanensa suke. Akwai babban fili tsakaninsu.
14 David cried out to the people, and to Abner, the son of Ner, saying, “Will you not respond, Abner?” And responding, Abner said, “Who are you, that you would cry out and disquiet the king?”
Sai Dawuda ya kira sojojin Shawulu da kuma Abner ɗan Ner ya ce, “Abner ba za ka amsa mini ba?” Abner ya ce, “Wane ne yake kira yana damun sarki haka?”
15 And David said to Abner: “Are you not a man? And who else is like you in Israel? Then why have you not guarded your lord the king? For one of the people entered, so that he might kill the king, your lord.
Dawuda ya ce wa Abner, “Wane irin mutum ne kai? Ba kai ne soja mafi iya yaƙi a Isra’ila ba? Don me ba ka yi gadin ranka yă daɗe, sarki da kyau ba? Ɗazu wani ya shiga tsakiyarku don yă kashe ranka yă daɗe, sarki.
16 This is not good, what you have done. As the Lord lives, you are sons of death, because you have not guarded your lord, the Christ of the Lord. Now therefore, where is the king’s spear, and where is the cup of water that was at his head?”
Abin da ka yi bai yi kyau ba. Muddin Ubangiji yana a raye kai da mutanenka kun cancanci mutuwa, domin ba ku lura da maigidanku shafaffe na Ubangiji ba. Ka duba kewaye da kai, ina māshi da kuma butar ruwan da suke kusa da kansa?”
17 Then Saul recognized the voice of David, and he said, “Is this not your voice, my son David?” And David said, “It is my voice, my lord the king.”
Shawulu ya gane muryar Dawuda, sai ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Dawuda ya ce, “I, muryata ce ya ranka yă daɗe, sarki.”
18 And he said: “For what reason has my lord pursued his servant? What have I done? Or what evil is there in my hand?
Ya ƙara da cewa, “Don me ranka yă daɗe, yake fafarata? Mene ne na yi? Wane abu ne aka same ni da laifi a kai?
19 Now therefore, listen, I beg you, my lord the king, to the words of your servant. If the Lord has stirred you up against me, let him make the sacrifice fragrant. But if the sons of men have done so, they are accursed in the sight of the Lord, who has cast me out this day, so that I would not live within the inheritance of the Lord, saying, ‘Go, serve strange gods.’
To, bari ranka yă daɗe, sarkina yă kasa kunne yă ji abin da zan faɗa. Idan Ubangiji ne ya sa ka yi fushi da ni, bari yă karɓi hadaya ta hatsi. Amma idan mutane ne suka sa ka, bari a la’anta su, Ubangiji ne shaidata. Gama sun kore ni don kada in sami rabo cikin gādon Ubangiji, suna cewa, ‘Ka je ka bauta wa waɗansu alloli.’
20 And now, let not my blood be poured out upon the earth before the Lord. For the king of Israel has gone out, so that he might seek a flea, just as the partridge is pursued amid the mountains.”
Kada ka yarda jinina yă zuba a ƙasa nesa da gaban Ubangiji. Sarkin Isra’ila ya fito yă nemi kuɗin cizo kamar mai farautar kazan duwatsu.”
21 And Saul said: “I have sinned. Return, my son David. For I will never again do evil to you, because my life has been precious in your eyes this day. For it is apparent that I have acted senselessly, and have been ignorant of very many things.”
Sai Shawulu ya ce, “Na yi zunubi ka dawo Dawuda ɗana. Ba zan yi maka kome ba, domin ka darajarta raina yau. Lalle na yi wawanci! Na yi babban kuskure.”
22 And responding, David said: “Behold, the king’s spear. Let one of the servants of the king cross over and take it.
Dawuda ya ce, “Ga māshin sarki, ka aiko wani saurayi yă zo yă karɓa.
23 And the Lord will repay each one according to his justice and faith. For the Lord has delivered you this day into my hand, but I was not willing to extend my hand against the Christ of the Lord.
Ubangiji yakan sāka wa kowa bisa ga adalcinsa da amincinsa. Ubangiji ya bashe ka a hannuna yau, amma ba zan sa hannuna a kan shafaffe na Ubangiji ba.
24 And just as your soul has been magnified this day in my eyes, so let my soul be magnified in the eyes of the Lord, and may he free me from all distress.”
Kamar yadda na ga darajar ranka yau. Haka ma bari Ubangiji yă ga darajar raina, yă cece ni daga dukan wahala.”
25 Then Saul said to David: “You are blessed, my son David. And whatever you may do, it shall certainly succeed.” And David departed on his way. And Saul returned to his place.
Sai Shawulu ya ce wa Dawuda, “Allah yă albarkace ka ɗana, Dawuda, za ka yi manyan abubuwa, tabbatacce kuma ka yi nasara.” Sai Dawuda ya yi tafiyarsa, Shawulu kuwa ya koma gida.

< 1 Samuel 26 >