< 1 Samuel 24 >

1 And when Saul had returned after pursuing the Philistines, they reported to him, saying, “Behold, David is in the desert of Engedi.”
Bayan da Shawulu ya komo daga fafaran Filistiyawa, sai aka gaya masa cewa, “Dawuda yana can a Jejin En Gedi.”
2 Therefore, Saul, taking three thousand elect men from all of Israel, traveled in order to search for David and his men, even upon the most broken rocks, which are passable only to mountain goats.
Saboda haka Shawulu ya zaɓi mutum dubu uku daga cikin dukan Isra’ila, suka fita neman Dawuda da mutanensa kusa da Duwatsun Awakin Jeji.
3 And he arrived at the sheepfolds, which presented themselves along the way. And a cave was in that place, which Saul entered, so that he might ease his bowels. But David and his men were hiding in the interior part of the cave.
Da Shawulu ya isa inda ake ajiye garken tumaki a bakin hanya inda akwai kogo, sai ya shiga ciki kogon don yă yi bayan gari. Dawuda da mutanensa kuwa suna can zaune a ƙurewar kogon.
4 And the servants of David said to him: “Behold the day, about which the Lord said to you, ‘I will deliver your enemy to you, so that you may do to him as it will be pleasing in your eyes.’” Then David rose up, and he quietly cut off the edge of Saul’s cloak.
Mutanen Dawuda suka ce, wannan rana ce Ubangiji ya yi magana ya ce maka, “Zan ba da maƙiyinka a hannunka domin ka yi abin da ka ga dama da shi.” Sai Dawuda ya tashi a hankali ya je ya yanke shafin rigar Shawulu.
5 After this, his own heart struck David, because he had cut off the edge of Saul’s cloak.
Daga baya Dawuda ya damu domin ya yanke shafin rigar Shawulu.
6 And he said to his men: “May the Lord be gracious to me, lest I do this thing to my lord, the Christ of the Lord, so that I lay my hand upon him. For he is the Christ of the Lord.”
Ya ce wa mutanensa, “Ubangiji yă sawwaƙe in yi abu haka ga shugabana da Ubangiji ya shafe, ko in ɗaga hannuna in kashe shi, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.”
7 And David restrained his men with his words, and he would not permit them to rise up against Saul. And so Saul, going out of the cave, continued to undertake his journey.
Da wannan magana Dawuda ya kwaɓi mutanensa, bai yarda su fāɗa wa Shawulu ba. Shawulu kuwa ya bar kogon ya yi tafiyarsa.
8 Then David also rose up after him. And departing from the cave, he cried out behind the back of Saul, saying: “My lord, the king!” And Saul looked behind him. And David, bowing himself face down to the ground, reverenced.
Daga baya Dawuda ya fita daga kogon sai ya kira Shawulu ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki!” Da Shawulu ya waiwaya, sai Dawuda ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
9 And he said to Saul: “Why do you listen to the words of men who say: ‘David seeks evil against you?’
Ya ce wa Shawulu, “Me ya sa kake saurari mutanen da suke cewa, ‘Dawuda ya dāge yă cuce ka’?
10 Behold, this day your eyes have seen that the Lord has delivered you into my hand, in the cave. And I thought that I might kill you. But my eye has spared you. For I said: I will not extend my hand against my lord, for he is the Christ of the Lord.
Yau ka ga da idonka yadda Ubangiji ya bashe ka a hannuna a cikin kogon nan. Waɗansu sun ce mini in kashe ka, amma na bar ka, na ce, ‘Ba zan sa hannuna a kan shugabana ba, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.’
11 Moreover, see and know, O my father, the edge of your cloak in my hand. For though I cut off the top of your cloak, I was not willing to extend my hand against you. Turn your soul and see that there is no evil in my hand, nor any iniquity or sin against you. Yet you lie in wait for my life, so that you may take it away.
Babana, duba, ga shafin rigarka a hannuna, na yanke shafin rigarka amma ban kashe ka ba. Yanzu ka gane ka kuma sani cewa ba ni da laifin aikata kome ko tayarwa, ban yi maka laifi ba, amma kana farautar raina.
12 May the Lord judge between me and you. And may the Lord vindicate me from you. But my hand will not be against you.
Ubangiji zai shari’anta tsakanina da kai. Ubangiji zai sāka mini laifin da ka yi mini, amma ni kam ba zan taɓa ka ba.
13 So too, it is said in the ancient proverb, ‘From the impious, impiety will go forth.’ Therefore, my hand will not be upon you.
Kamar yadda karin maganan nan na dā ya ce, ‘Daga cikin masu mugunta, mugunta ke fitowa,’ hannuna dai ba zai taɓa ka ba.
14 Whom are you pursuing, O king of Israel? Whom are you pursuing? You are pursuing a dead dog, a single flea.
“Wane ne sarkin Isra’ila, ka fito kake bi? Wa kake kora? Kana bin mataccen kare ko kuɗin cizo?
15 May the Lord be the judge, and may he judge between me and you. And may he see and judge my case, and rescue me from your hand.”
Ubangiji yă zama alƙali, yă yi shari’a tsakanina da kai, bari Ubangiji yă duba, yă tsaya mini, yă nuna ba ni da laifi.”
16 And when David had completed speaking words in this way to Saul, Saul said, “Could this be your voice, my son David?” And Saul lifted up his voice, and he wept.
Da Dawuda ya gama wannan magana, sai Shawulu ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Sai ya fasa da kuka.
17 And he said to David: “You are more just than I am. For you have distributed good to me, but I have repaid evil to you.
Ya ce, “Ka fi ni gaskiya, ka yi mini alheri, ni kuwa na yi maka mugunta.
18 And you have revealed this day the good that you have done for me: how the Lord delivered me into your hand, but you did not kill me.
Ga shi yanzu ka faɗa mini alherin da ka yi mini. Ubangiji ya bashe ni a hannunka amma ba ka kashe ni ba.
19 For who, when he will have found his enemy, will release him along a good path? So may the Lord repay you for this good turn, because you have acted on my behalf this day.
In mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi yă tafi lafiya ba tare da yin masa rauni ba? Ubangiji yă sāka maka, gama ka nuna mini alheri a yau.
20 And now I know certainly that you shall be king, and you shall have the kingdom of Israel in your hand.
Na sani tabbatacce za ka zama sarki. Masarautar Isra’ila za tă kahu a hannunka.
21 Swear to me in the Lord that you will not take away my offspring after me, nor take away my name from the house of my father.”
Yanzu ka rantse mini da Ubangiji cewa ba za ka hallaka zuriyarta ko ka share sunana daga iyalin mahaifina ba.”
22 And David swore to Saul. Therefore, Saul went away to his own house. And David and his men ascended to places that were more secure.
Sai Dawuda ya rantse wa Shawulu. Sa’an nan Shawulu ya koma gida, amma Dawuda da mutanensa suka haura zuwa wurin ɓuya.

< 1 Samuel 24 >