< 1 Samuel 22 >

1 Then David went away from there, and he fled to the cave of Adullam. And when his brothers and all of his father’s house had heard of it, they descended to him there.
Dawuda ya bar Gat, ya tsere zuwa kogon Adullam. Da’yan’uwansa da kuma iyalan mahaifinsa suka ji labari, sai suka tafi can wurinsa.
2 And all those left in distress, or oppressed by debt to strangers, or bitter in soul, gathered themselves to him. And he became their leader, and about four hundred men were with him.
Dukan mutanen da suke cikin wahala, da waɗanda ake binsu bashi, da masu damuwoyi, suka tattaru a wurin Dawuda. Shi kuwa ya zama shugabansu. Yawansu ya kai ɗari huɗu.
3 And David set out from there to Mizpah, which is of Moab. And he said to the king of Moab, “I beg you, let my father and my mother remain with you, until I know what God will do for me.”
Daga can Dawuda ya tafi Mizfa a Mowab. Ya ce wa sarkin Mowab, “Za ka yarda mahaifina da mahaifiyata su zo su zauna a wurinka kafin in san abin da Allah zai yi da ni?”
4 And he left them before the face of the king of Moab. And they stayed with him for all the days that David was in the stronghold.
Saboda haka ya bar su a wurin sarkin Mowab, suka zauna da shi duk tsawon lokacin da Dawuda yake ta ɓuya a kogwannin duwatsu.
5 And the prophet Gad said to David: “Do not choose to stay in the stronghold. Set out and go into the land of Judah.” And so, David set out, and he went into the forest of Hereth.
Amma annabin nan Gad ya ce wa Dawuda, “Kada ka zauna a nan, maza ka tashi ka shiga ƙasar Yahuda”. Sai Dawuda ya tashi ya tafi jejin Heret.
6 And Saul heard that David, and the men who were with him, had been seen. Now while Saul was staying in Gibeah, and while he was in the forest that is in Ramah, holding a spear in his hand, with all his servants standing around him,
Sai Shawulu ya sami labari cewa an ga Dawuda da mutanensa. Shawulu kuwa yana zaune da māshinsa kusa a ƙarƙashin itacen tsamiya a tudun Gibeya, tare da dukan ma’aikatansa kewaye da shi.
7 he said to his servants who were assisting him: “Listen now, you sons of Benjamin! Will the son of Jesse give to all of you fields and vineyards, and will he make all of you tribunes or centurions,
Ya ce musu, “Mutanen Benyamin, ku saurara; ɗan Yesse zai iya ba dukanku filaye da gonakin inabi ne? Zai ba dukanku shugabanci na dubbai ko shugabanci na ɗari-ɗari?
8 so that you would all conspire against me, and so that there is no one to inform me, especially when even my son has formed a pact with the son of Jesse? There is no one among you who grieves for my situation, or who would report to me. For my son has raised up my servant against me, seeking to betray me, even to this day.”
Abin da ya sa dukanku kuka gama baki a kaina? Ba wanda ya gaya mini lokacin da ɗana ya yi yarjejjeniya da ɗan Yesse, ba wanda ya kulla da ni, ko ya gaya mini cewa ɗana ya sa bawana yă tayar mini, yana fakona kamar yadda yake a yau.”
9 Then Doeg, the Edomite, who was standing near, and who was first among the servants of Saul, responding, said: “I saw the son of Jesse, in Nob, with Ahimelech, the son of Ahitub, the priest.
Amma Doyeg mutumin Edom da yake tsaye tare da fadawan Shawulu ya ce, “Na ga ɗan Yesse ya zo wurin Ahimelek ɗan Ahitub a Nob.
10 And he consulted the Lord for him, and he gave him food. Moreover, he gave him the sword of Goliath, the Philistine.”
Ahimelek ya roƙi Ubangiji saboda shi, ya kuma ba shi guzuri da takobin Goliyat Bafilistin.”
11 Then the king sent to summon Ahimelech, the priest, the son of Ahitub, and all of his father’s house, the priests who were in Nob, and they all came before the king.
Sai sarki ya aika aka kira masa Ahimelek firist ɗan Ahitub da dukan iyalin mahaifinsa. Dukansu suka zo wurin sarki.
12 And Saul said to Ahimelech, “Listen, son of Ahitub.” He responded, “Here I am, lord.”
Shawulu ya ce, “Ka saurara yanzu, ɗan Ahitub.” Ya amsa ya ce, “Ina saurara, ranka yă daɗe.”
13 And Saul said to him: “Why have you conspired against me, you and the son of Jesse? For you gave him bread and a sword, and you consulted the Lord for him, so that he might rise up against me, continuing as a traitor even to this day.”
Shawulu ya ce masa, “Don me ka gama baki da ɗan Yesse a kaina har ka ba shi burodi da takobin (Goliyat), ka kuma roƙi Allah don yă tayar mini, yă kuma yi fakona kamar yadda yake yi yau?”
14 And responding to the king, Ahimelech said: “But who among all your servants is as faithful as David? And he is the son-in-law of the king, and he goes forth at your order, and he is a glory within your house.
Ahimelek ya ce wa sarki, “A cikin bayinka duka, wa ke da aminci iri na Dawuda, surukin sarki, shugaban jarumanka wanda ake girmamawa da gaske a gidanka?
15 Did I begin to consult the Lord for him today? May this be far from me! Let not the king suspect this kind of thing against his servant, nor against anyone in all my father’s house. For your servant did not know anything about this matter, either small or great.”
A wannan rana ce da na fara roƙon Allah saboda shi? Kada sarki yă zargi bawansa ko wani daga iyalin mahaifinsa, gama bawanka bai san kome a kan dukan waɗannan al’amura ba.”
16 And the king said, “You shall die a death, Ahimelech, you and all your father’s house!”
Amma sarki ya ce, “Lalle Ahimelek za ka mutu, da kai da dukan iyalin mahaifinka.”
17 And the king said to the emissaries who were standing around him: “You shall turn, and put to death the priests of the Lord. For their hand is with David. They knew that he had fled, and they did not reveal it to me.” But the servants of the king were not willing to extend their hands against the priests of the Lord.
Sai sarki ya umarci matsaran da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Ku kakkashe firistocin Ubangiji, gama su ma sun goyi bayan Dawuda. Sun san yana gudu, duk da haka ba su gaya mini ba.” Amma ma’aikatan sarki ba su yarda su sa hannu su kashe firistocin Ubangiji ba.
18 And the king said to Doeg, “You shall turn and rush against the priests.” And Doeg, the Edomite, turned and rushed against the priests. And he massacred, on that day, eighty-five men, vested with the linen ephod.
Sai sarki ya umarce Doyeg ya ce, “Ka juya ka kakkashe firistocin.” Doyeg mutumin Edom ya juya ya kakkashe firistocin. A ranar kuwa ya kashe mutum tamanin da biyar waɗanda suke sanye da efod na lilin.
19 Then he struck Nob, the city of the priests, with the edge of the sword; he struck down men and women, little ones and infants, as well as ox and donkey and sheep, with the edge of the sword.
Ya kuma hallaka Nob birnin firistoci, ya kashe dukan mata, da maza, da yara, da jarirai, da shanu, da jakuna, da kuma tumaki.
20 But one of the sons of Ahimelech, the son of Ahitub, whose name was Abiathar, escaping, fled to David.
Amma Abiyatar ɗan Ahimelek jikan Ahitub ya tsere, ya gudu zuwa wurin Dawuda.
21 And he reported to him that Saul had slain the priests of the Lord.
Abiyatar gaya wa Dawuda cewa, “Shawulu ya hallaka firistocin Ubangiji.”
22 And David said to Abiathar: “I knew, on that day when Doeg, the Edomite was there, that without doubt he would report it to Saul. I am guilty of all the souls of your father’s house.
Dawuda ya ce wa Abiyatar, “Lalle a wancan ranar, sa’ad da na ga Doyeg mutumin Edom a can, na san tabbatacce zai gaya wa sarki. Ni ne sanadin mutuwar dukan iyalin mahaifinka.
23 You should remain with me. Do not be afraid. For he who seeks my life, seeks your life also, but with me you shall be saved.”
Ka zauna tare da ni, kada ka ji tsoro mutumin da yake neman ranka, yana nema raina ma. Ka zauna lafiya tare da ni.”

< 1 Samuel 22 >