< 1 Samuel 18 >

1 And it happened that, when he had completed speaking to Saul, the soul of Jonathan adhered to the soul of David, and Jonathan loved him like his own soul.
Bayan da Dawuda ya gama magana da Shawulu, sai Yonatan ɗan Shawulu ya ji zuciyarsa tana son Dawuda sosai. Yonatan kuwa yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
2 And Saul took him that day, and would not permit him to return to his father’s house.
Tun daga wannan rana Shawulu ya zaunar da Dawuda tare da shi, bai bar shi ya koma gidan mahaifinsa ba.
3 Then David and Jonathan formed a pact. For he loved him like his own soul.
Yonatan kuma ya yi yarjejjeniya da Dawuda saboda yana ƙaunarsa kamar ransa.
4 And Jonathan took off the coat that he was wearing, and he gave it to David, with the rest of his garments, even to his sword and bow, and even his belt.
Yonatan ya tuɓe doguwar taguwarsa da ya sa, ya ba wa Dawuda, tare da sulkensa, har ma da māshi da kibiyarsa, da kuma bel nasa.
5 Also, David went out to do everything whatsoever that Saul sent him to do, and he conducted himself prudently. And Saul set him over men of war. And he was acceptable in the eyes of the entire people, and most of all in the sight of the servants of Saul.
Duk abin da Shawulu ya aiki Dawuda yă yi yakan yi shi cikin aminci, har Shawulu ya ba shi babban makami a rundunarsa. Wannan ya faranta wa dukan mutane zuciya har ma da ma’aikatan Shawulu.
6 Now when David returned, after he had struck down the Philistine, the women went out, from all the cities of Israel, leading the singing and dancing, rejoicing with timbrels and bells, so as to meet king Saul.
Yayinda mutane suke dawowa gida bayan da Dawuda ya kashe Bafilistin, mata suka fito daga dukan biranen Isra’ila don su sadu da Sarki Shawulu, suna waƙoƙi da raye-raye masu farin ciki, da ganguna da sarewa.
7 And the women sang, as they played, saying, “Saul has struck down a thousand, and David ten thousand.”
Suna rawa suna cewa, “Shawulu ya kashe dubbansa, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai.”
8 Then Saul became exceedingly angry, and this word was displeasing in his eyes. And he said: “They have given David ten thousand, and to me they gave only one thousand. What is left for him, except the kingdom itself?”
Shawulu kuwa ya ji fushi, wannan magana ba tă yi masa daɗi ba, ya yi tunani ya ce, “Suna yabon Dawuda cewa ya kashe dubun dubbai amma ni dubbai kawai. Me ya rage masa yanzu, in ba mulki ba?”
9 Therefore, Saul did not regard David with a good eye, from that day and thereafter.
Tun daga wannan lokaci zuwa gaba, Shawulu ya dinga kishin Dawuda.
10 Then, on the next day, the evil spirit from God assailed Saul, and he prophesied in the midst of his house. And David played with his hand, just as at every other time. And Saul held a lance in his hand.
Kashegari, mugun ruhu daga Allah ya fāɗo wa Shawulu da tsanani. Yana annabci a gidansa, Dawuda kuwa yana bugan molo kamar yadda ya saba. Shawulu yana riƙe da māshi a hannunsa.
11 And he threw it, thinking that he would be able to fix David to the wall. And David stepped aside twice, from before his face.
Da ƙarfi yana magana da kansa yana cewa, “Zan kafe Dawuda da bango.” Amma Dawuda ya bauɗe masa sau biyu.
12 And Saul feared David, because the Lord was with him, but he had withdrawn from Saul.
Shawulu ya ji tsoron Dawuda don Ubangiji yana tare da shi, amma Ubangiji ya riga ya bar Shawulu.
13 Therefore, Saul sent him away from himself, and he made him tribune over one thousand men. And he entered and departed in the sight of the people.
Saboda haka Shawulu bai yarda Dawuda yă zauna tare da shi ba, amma ya maishe shi shugaban sojoji dubu. Dawuda kuwa ya riƙa bi da su yana kaiwa yana kuma da tare da su.
14 Also, David acted prudently in all his ways, and the Lord was with him.
A kome da Dawuda ya yi yakan yi nasara gama Ubangiji yana tare da shi.
15 And so, Saul saw that he was exceedingly prudent, and he began to be wary of him.
Da Shawulu ya ga yadda yake cin nasara, sai ya ji tsoronsa.
16 But all of Israel and Judah loved David. For he entered and departed before them.
Amma dukan Isra’ila da Yahuda suka ƙaunaci Dawuda gama yana bin da su a yaƙe-yaƙensu.
17 And Saul said to David: “Behold, my elder daughter, Merab. I will give her to you as wife. Only be a valiant man, and fight the wars of the Lord.” Now Saul was considering within himself, saying, “Let not my hand be upon him, but let the hands of the Philistines be upon him.”
Shawulu ya ce wa Dawuda, “Ga diyata Merab zan ba ka ka aura, kai dai ka yi mini aiki da himma, ka kuma yi yaƙe-yaƙen Ubangiji.” Saboda Shawulu ya ce wa kansa, “Ba zan ɗaga hannuna a kansa ba, Filistiyawa ne za su yi wannan.”
18 Then David said to Saul, “Who am I, and what is my life, and what is my father’s kinship within Israel, that I should be the son-in-law of the king?”
Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Wane ni, wa ya san iyayena ko kabilar iyayena a Isra’ila da zan zama surukin sarki?”
19 Then it happened that, at the time when Merab, the daughter of Saul, was to be given to David, she was given to Adriel, the Meholathite, as wife.
Da lokaci ya kai da Merab’yar Shawulu za tă yi aure da Dawuda, sai aka aurar da ita wa Adriyel na Mehola.
20 Now Michal, the other daughter of Saul, loved David. And this was reported to Saul, and it pleased him.
Mikal’yar Shawulu kuwa tana ƙaunar Dawuda sosai. Da aka gaya wa Shawulu labarin, sai ya yi farin ciki, ya yi tunani ya ce,
21 And Saul said, “I will give her to him, so that she may be a stumbling block to him, and so that the hand of the Philistines may be upon him.” And Saul said to David, “In two things, you shall be my son-in-law today.”
“Zan ba shi ita tă zama masa tarko, da haka Filistiyawa za su same shi.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Yanzu kana da dama sau na biyu ka zama surukina.”
22 And Saul commanded his servants to speak to David privately, saying: “Behold, you are pleasing to the king, and all his servants love you. Now therefore, be the son-in-law of the king.”
Sai Shawulu ya umarci ma’aikatansa cewa, “Ku yi magana da Dawuda asirce ku ce, ‘Duba, sarki yana farin ciki da kai, dukan ma’aikatansa kuma suna sonka, ka yarda ka zama surukinsa.’”
23 And the servants of Saul spoke all these words to the ears of David. And David said: “Does it seem a small matter to you, to be the son-in-law of the king? I am but a poor and unimportant man.”
Suka sāke yi wa Dawuda wannan magana amma Dawuda ya ce, “Kuna tsammani abu mai sauƙi ne mutum yă zama surukin sarki? Ni talaka ne, kuma ba sananne ba.”
24 And the servants reported to Saul, saying, “David has spoken words in this manner.”
Da ma’aikatan Shawulu suka gaya masa abin da Dawuda ya faɗa.
25 Then Saul said, “Speak in this way to David: The king does not have need of any dowry, but only one hundred foreskins from the Philistine men, so that he may be vindicated from the enemies of the king.” So did Saul think to deliver David into the hands of the Philistines.
Sai Shawulu ya ce, “Ku gaya wa Dawuda, ‘Sarki ba ya bukatan kuɗin auren’yarsa, sai dai loɓar Filistiyawa domin ramako a kan abokan gābansa.’” Shawulu yana shiri ne domin Dawuda yă fāɗa a hannun Filistiyawa.
26 And when his servants had repeated to David the words that Saul had spoken, the word was pleasing in the eyes of David, so that he would become son-in-law of the king.
Da ma’aikatan suka gaya wa Dawuda waɗannan abubuwa, sai ya yi murna don zai zama surukin sarki. Amma kafin lokacin yă cika,
27 And after a few days, David, rising up, went with the men who were under him, and he struck down two hundred men of the Philistines. And he brought their foreskins, and he counted them out for the king, so that he might be his son-in-law. And so, Saul gave to him his daughter Michal as wife.
Dawuda da mutanensa suka fita suka kashe Filistiyawa ɗari biyu, suka kawo loɓar suka miƙa wa sarki, domin yă zama surukin sarki. Sai Shawulu ya ba da’yarsa Mikal aure ga Dawuda.
28 And Saul saw and understood that the Lord was with David. And Michal, the daughter of Saul, loved him.
Da Shawulu ya gane Ubangiji yana tare da Dawuda,’yarsa Mikal kuma tana ƙaunarsa,
29 And Saul began to fear David all the more. And Saul became the enemy of David, every day.
sai Shawulu ya ƙara jin tsoron Dawuda har ya zama maƙiyinsa a dukan sauran rayuwarsa.
30 And the leaders of the Philistines departed. And from the beginning of their departure, David conducted himself more prudently than all the servants of Saul, and his name became exceedingly celebrated.
Manyan sojojin Filistiyawa suka yi ta fita suna yaƙi da Isra’ilawa, amma kullum Dawuda yakan sami nasara fiye da sauran manyan sojojin Shawulu. Ta haka ya yi suna ƙwarai.

< 1 Samuel 18 >