< 1 Kings 8 >

1 Then all those greater by birth of Israel, with the leaders of the tribes and the rulers of the families of the sons of Israel, gathered together before king Solomon at Jerusalem, so that they might carry the ark of the covenant of the Lord, from the city of David, that is, from Zion.
Sai Sarki Solomon ya tattara dattawan Urushalima a gabansa, da dukan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalan Isra’ilawa, domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
2 And all of Israel assembled before king Solomon, on the solemn day in the month of Ethanim, which is the seventh month.
Dukan mutanen Isra’ila suka tattaru a gaban Sarki Solomon a lokacin biki, a watan Etanim, wato, wata na bakwai.
3 And all the elders of Israel arrived, and the priests took up the ark.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin,
4 And they carried the ark of the Lord, and the tabernacle of the covenant, and all the vessels of the Sanctuary, which were in the tabernacle; and the priests and the Levites carried these.
suka haura da akwatin alkawarin Ubangiji da kuma Tentin Sujada, da dukan kayayyaki masu tsarkin da suke cikinsa. Firistoci da Lawiyawa suka ɗauko su,
5 Then king Solomon, and the entire multitude of Israel, who had assembled before him, advanced with him before the ark. And they immolated sheep and oxen, which could not be numbered or estimated.
sai Sarki Solomon da dukan taron Isra’ila da suka tattaru kewaye da shi a gaban akwatin alkawari, suka yi ta miƙa hadayar tumaki da bijimai masu yawa da ba a iya lissaftawa, ko ƙirgawa.
6 And the priests brought in the ark of the covenant of the Lord to its place, into the oracle of the temple, in the Holy of Holies, under the wings of the cherubim.
Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji inda aka shirya masa, can ciki cikin haikali, a Wuri Mafi Tsarki, aka kuma sa shi a ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
7 For indeed, the cherubim extended their wings over the place of the ark, and they protected the ark and its bars from above.
Kerubobin sun buɗe fikafikansu a bisa wurin da akwatin alkawarin yake, suka inuwartar da akwatin alkawarin da sandunan ɗaukansa.
8 And since the bars projected outward, their ends were visible from without, in the Sanctuary before the oracle; but they were not visible farther outward. And they have been in that place even to the present day.
Waɗannan sandunan sun yi tsawo har ana iya ganin bakinsu daga Wuri Mai Tsarki a gaban wuri mai tsarki na can ciki, amma ba a iya ganinsu daga waje na Wuri Mai Tsarki ba. Suna nan kuwa a can har wa yau.
9 Now inside the ark, there was nothing other than the two tablets of stone, which Moses had placed in it at Horeb, when the Lord formed a covenant with the sons of Israel, when they departed from the land of Egypt.
Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
10 Then it happened that, when the priests had exited from the Sanctuary, a cloud filled the house of the Lord.
Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
11 And the priests were unable to stand and minister, because of the cloud. For the glory of the Lord had filled the house of the Lord.
Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
12 Then Solomon said: “The Lord has said that he would dwell in a cloud.
Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
13 Building, I have built a house as your dwelling place, your most firm throne forever.”
ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
14 And the king turned his face, and he blessed the entire assembly of Israel. For the entire assembly of Israel was standing.
Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsattsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
15 And Solomon said: “Blessed is the Lord, the God of Israel, who spoke with his mouth to my father David, and who, with his own hands, has perfected it, saying:
Sa’an nan ya ce, “Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannunsa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
16 ‘From the day when I led my people Israel away from Egypt, I did not choose any city out of all the tribes of Israel, so that a house would be built, and so that my name might be there. Instead, I chose David to be over my people Israel.’
‘Tun ran da na fitar da mutanena Isra’ila daga Masar, ban zaɓi wani birni a cikin wata kabilar Isra’ila a gina haikali domin Sunana yă kasance a can ba, amma na zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
17 And my father David wanted to build a house to the name of the Lord, the God of Israel.
“Mahaifina Dawuda ya yi niyya a cikin zuciyarsa yă gina haikali saboda Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
18 But the Lord said to my father David: ‘Since you have planned in your heart to build a house to my name, you have done well by considering this plan in your mind.
Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Saboda yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka yi niyyar wannan a zuciyarka.
19 Yet truly, you shall not build a house for me. Instead, your son, who shall go forth from your loins, he himself shall build a house to my name.’
Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikali, amma ɗanka, wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
20 The Lord has confirmed his word which he spoke. And so I stand in place of my father David, and I sit upon the throne of Israel, just as the Lord said. And I have built a house to the name of the Lord, the God of Israel.
“Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina, yanzu kuma ga shi na zauna a kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya yi alkawari, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
21 And there I have appointed a place for the ark, in which is the covenant of the Lord that he struck with our fathers, when they went forth from the land of Egypt.”
Na tanada wuri saboda akwatin alkawari, akwatin da ya ƙunshi alkawarin da Ubangiji ya yi da kakanninmu sa’ad da ya fitar da su daga Masar.”
22 Then Solomon stood before the altar of the Lord, in the sight of the assembly of Israel, and he extended his hands toward heaven.
Sai Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji, a gaban dukan taron Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,
23 And he said: “Lord God of Israel, there is no God like you, in heaven above, nor on the earth below. You preserve covenant and mercy with your servants, who walk before you with all their heart.
ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama can bisa, ko a ƙasa can ƙarƙashi, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna ga bayinka waɗanda suke cin gaba a hanyarka da dukan zuciyarsu.
24 You have fulfilled, for your servant David, my father, that which you said to him. With your mouth, you spoke; and with your hands, you completed; just as this day proves.
Ka kiyaye alkawarinka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina. Da bakinka ka yi alkawari, da hannunka kuma ka cika shi, yadda yake a yau.
25 Now therefore, O Lord God of Israel, fulfill, for your servant David, my father, that which you spoke to him, saying, ‘There shall not be taken away from you a man before me, who may sit upon the throne of Israel, if only your sons will guard their way, so that they walk before me, just as you have walked in my sight.’
“Yanzu, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari ka cika wa bawanka Dawuda mahaifina alkawaran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza sun yi hankali cikin dukan abubuwan da suke yi, don su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi.’
26 And now, O Lord God of Israel, establish your words, which you spoke to your servant David, my father.
Yanzu fa, ya Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina tă cika.
27 Is it, then, to be understood that truly God would dwell upon the earth? For if heaven, and the heavens of heavens, are not able to contain you, how much less this house, which I have built?
“Amma anya, Allah, za ka zauna a duniya? Sammai, har ma da saman sammai ba za tă iya riƙe ka ba, balle wannan haikalin da na gina!
28 Yet look with favor upon the prayer of your servant and upon his petitions, O Lord, my God. Listen to the hymn and the prayer, which your servant prays before you this day,
Duk da haka ka ji addu’ar bawanka da kuma roƙonsa don jinƙai, ya Ubangiji Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka a wannan rana.
29 so that your eyes may be open over this house, night and day, over the house about which you said, ‘My name shall be there,’ so that you may heed the prayer that your servant is praying in this place to you.
Bari idanunka su buɗe, su fuskanci wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce, ‘Sunana zai kasance a can,’ saboda ka ji addu’ar bawanka in yana fuskantar wannan wuri.
30 So may you heed the supplication of your servant and of your people Israel, whatever they will pray for in this place, and so may you heed them in your dwelling place in heaven. And when you heed, you will be gracious.
Ka ji roƙon bawanka da kuma na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a, suka fuskanci wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka, kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
31 But if any man sins against his neighbor, and he has any kind of an oath by which he is bound, and he arrives because of the oath, before your altar in your house,
“Sa’ad da mutum ya yi abin da ba daidai ba ga maƙwabcinsa, an kuma bukace shi yă yi rantsuwa, sai ya zo ya rantse a gaban bagade a cikin haikalin nan,
32 you will hear in heaven, and you will act and judge your servants, condemning the impious, and repaying his own way upon his own head, but justifying the just, and rewarding him in accord with his justice.
sai ka ji daga sama, ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, ka hukunta mai laifi, ka mai da laifinsa a kansa, mai gaskiya kuma ka nuna shi marar laifi ne bisa ga gaskiyarsa.
33 And if your people Israel will have fled from their enemies, because they have sinned against you, and doing penance and confessing to your name, shall arrive and pray and petition you in this house,
“Sa’ad da abokan gāba suka ci mutanenka Isra’ila a yaƙi saboda sun yi maka zunubi, sa’ad da kuma suka dawo gare ka don su furta sunanka, suna addu’a suna roƙo gare ka a wannan haikali,
34 listen in heaven, and forgive the sin of your people Israel, and lead them back to the land, which you gave to their fathers.
ka ji daga sama, ka gafarta zunubin mutanenka, ka kuma dawo da su ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
35 And if the heavens have closed, so that there is no rain, because of their sins, and they, praying in this place, shall do penance to your name, and shall be converted from their sins, by occasion of their afflictions,
“Sa’ad da sammai sun kulle, babu kuma ruwan sama domin mutane sun yi maka zunubi, sa’ad da suka yi addu’a suna fuskantar wannan wuri, suka kuma furta sunanka, suka juye daga zunubinsu domin ka hore su,
36 hear them from heaven, and forgive the sins of your servants and of your people Israel. And reveal to them the good way, along which they should walk, and grant rain upon your land, which you have given to your people as a possession.
ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.
37 Then, if famine rises over the land, or pestilence, or corrupt air, or blight, or locust, or mildew, or if their enemy afflicts them, besieging the gates, or any harm or infirmity,
“Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, ko kuwa abokan gāba sun yi musu kwanto, a wani daga cikin biranensu, duk wata cuta, ko ciwon da ya zo,
38 or whatever curse or divine intervention may happen to any man among your people Israel, if anyone understands, having been wounded in his heart, and if he will have extended his hands in this house,
in suka yi addu’a ko roƙo ta wurin wani daga cikin mutanenka Isra’ila, kowa ya san wahalar zuciyarsa, ya kuma buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali,
39 you will hear in heaven, in your dwelling place, and you will forgive. And you will act so that you give to each one in accord with his own ways, just as you see in his heart, for you alone know the heart of all the sons of men.
sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi wani abu. Ka yi da kowane mutum bisa ga dukan abin da ya yi, tun da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan dukan mutane),
40 So may they fear you, all the days that they live upon the face of the land, which you have given to our fathers.
saboda su ji tsoronka a kowane lokacin da suke zaune a ƙasar da ka ba wa kakanninmu.
41 Moreover, the foreigner too, who is not of your people Israel, when he will have arrived from a distant land because of your name, for they shall hear about your great name, and your strong hand,
“Game da baƙo kuwa wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba, amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka,
42 and your outstretched arm everywhere: so when he arrives and prays in this place,
gama mutane za su ji game da girman sunanka, da ƙarfin hannunka, da kuma hannunka mai iko, sa’ad da ya zo, ya yi addu’a yana fuskantar wannan haikali,
43 you will listen in heaven, in the firmament of your dwelling place. And you will do all the things, for which that foreigner will have called upon you. So may all the peoples of the earth learn to fear your name, just as your people Israel do. And so may they show that your name has been invoked over this house, which I have built.
ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi dukan abin da baƙon ya tambaye ka, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, bari kuma su san cewa wannan gidan da na gina, ya amsa Sunanka.
44 And if your people have gone out to war against their enemies, along whatever way you will send them, they shall pray to you in the direction of the city, which you have chosen, and toward the house, which I have built to your name.
“Sa’ad da mutanenka suka tafi yaƙi da abokan gābansu, a duk inda ka aike su, sa’ad da kuma suka yi addu’a ga Ubangiji suna fuskantar birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka,
45 And you will hear in heaven their prayers and their petitions. And you will accomplish judgment for them.
ka ji addu’arsu da roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatansu.
46 But if they sin against you, for there is no man who does not sin, and you, being angry, deliver them to their enemies, and they will have been led away as captives to the land of their enemies, whether far or near,
“Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su, ka kuma ba da su ga abokin gāba, wanda ya kwashe su kamammu zuwa ƙasarsa, nesa ko kusa;
47 and if they do penance in their heart, in the place of captivity, and having been converted, make supplication to you in their captivity, saying, ‘We have sinned; we acted unjustly; we committed impiety,’
in suka canja zuciyarsu a ƙasar da aka riƙe su kamammu, suka tuba, suka kuma roƙe ka a ƙasar waɗanda suka ci su da yaƙi, suka ce, ‘Mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba, mun yi mugunta’;
48 and they return to you with all their heart and all their soul, in the land of their enemies, to which they have been led away as captives, and if they pray to you in the direction of their land, which you gave to their fathers, and of the city, which you have chosen, and of the temple, which I have built to your name:
in sun juye gare ka da dukan zuciyarsu, da dukan ransu a ƙasar abokan gābansu waɗanda suka kwashe kamammu, suka yi addu’a gare ka, suka fuskanci wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, waje birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka;
49 you will hear in heaven, in the firmament of your throne, their prayers and their petitions. And you will accomplish their judgment.
sai ka ji daga sama, mazauninka, ka ji addu’a da roƙonsu, ka kuma biya musu bukatansu.
50 And you will forgive your people, who have sinned against you, and all their iniquities, by which they have transgressed against you. And you will grant to them mercy in the sight of those who have made them captives, so that they may take pity on them.
Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi; ka gafarta dukan laifofin da suka yi maka, ka kuma sa waɗanda suka ci su a yaƙi su ji tausayinsu.
51 For they are your people and your inheritance, whom you have led away from the land of Egypt, from the midst of the furnace of iron.
Gama su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fitar daga Masar, daga tanderu mai narken ƙarfe.
52 So may your eyes be open to the supplication of your servant and of your people Israel. And so may you heed them in all the things about which they will call upon you.
“Bari idanunka su buɗe ga roƙon bawanka, ga roƙon mutanenka Isra’ila, bari kuma ka saurare su sa’ad da suka yi kuka gare ka.
53 For you have separated them to yourself as an inheritance, from among all the peoples of the earth, just as you spoke by Moses, your servant, when you led our fathers away from Egypt, O Lord God.”
Gama ka ware su daga dukan al’umman duniya su zama abin gādonka, kamar yadda aka furta ta wurin bawanka Musa sa’ad da kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka ka fitar da kakanninmu daga Masar.”
54 And it happened that, when Solomon had completed praying this entire prayer and supplication to the Lord, he rose up from the sight of the altar of the Lord. For he had fixed both knees upon the ground, and he had extended his hands toward heaven.
Da Solomon ya gama dukan waɗannan addu’o’i da roƙe-roƙe ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda ya durƙusa da hannuwansa a buɗe waje sama.
55 Then he stood and blessed the entire assembly of Israel in a great voice, saying:
Ya tashi ya kuma albarkaci dukan taron Isra’ila da babbar murya, yana cewa,
56 “Blessed is the Lord, who has given rest to his people Israel, in accord with all that he said. Not even one word, out of all the good things that he spoke by his servant Moses, has fallen away.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya ba wa mutanensa hutu kamar dai yadda ya yi alkawari. Babu magana guda da ta kāsa cika cikin dukan alkawaransa masu kyau da ya yi ta wurin bawansa Musa.
57 May the Lord our God be with us, just as he was with our fathers, not abandoning us, and not rejecting us.
Bari Ubangiji Allah yă kasance tare da mu kamar yadda ya kasance da kakanninmu; kada yă taɓa rabu da mu, ko yă yashe mu.
58 But may he incline our hearts to himself, so that we may walk in all his ways, and keep his commandments, and his ceremonies, and whatever judgments he commanded to our fathers.
Bari yă juye zukatanmu gare shi, don mu yi tafiya a cikin dukan hanyoyinsa, mu kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa, da kuma farillan da ya ba wa kakanninmu.
59 And may these my words, by which I have prayed before the Lord, be near to the Lord our God, day and night, so that he may accomplish judgment for his servant and for his people Israel, throughout each day.
Bari kuma waɗannan kalmomina, waɗanda na yi addu’a a gaban Ubangiji, su yi kusa da Ubangiji Allahnmu, dare da rana, don yă biya bukatan bawansa da na mutanensa Isra’ila, bisa ga bukatan kowa,
60 So may all the peoples of the earth know that the Lord himself is God, and there is no other beside him.
saboda dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji, shi ne Allah, babu kuma wani.
61 Also, may our hearts be perfect with the Lord our God, so that we may walk in his decrees, and keep his commandments, as also on this day.”
Amma dole ku miƙa zukatanku ga Ubangiji Allahnmu, don ku rayu, ta wurin bin ƙa’idodinsa, ku kuma yi biyayya da umarnansa, kamar yadda kuke yi a wannan lokaci.”
62 Then the king, and all of Israel with him, immolated victims before the Lord.
Sai sarki da dukan Isra’ila, suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
63 And Solomon slew sacrifices of peace offerings, which he immolated to the Lord: twenty-two thousand oxen, and twenty thousand one hundred sheep. And the king and all the sons of Israel dedicated the temple of the Lord.
Solomon ya miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, shanu dubu ashirin da biyu, tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan Isra’ilawa suka keɓe haikalin Ubangiji.
64 On that day, the king sanctified the middle of the atrium, which was before the house of the Lord. For in that place, he offered holocaust, and sacrifice, and the fat of peace offerings. For the bronze altar, which was before the Lord, was too small and was not able to hold the holocaust, and the sacrifice, and the fat of the peace offerings.
A wannan rana sarki ya tsarkake sashe na tsakiyar fili a gaban haikalin Ubangiji, a can kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, da kitsen hadaya ta salama, gama bagaden tagulla a gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta sosai da za a miƙa hadayun ƙonawa, hadayun hatsi, da kuma kitsen hadayun salama.
65 Then Solomon made, at that time, a celebratory festival, and all of Israel with him, a great multitude, from the entrance of Hamath to the river of Egypt, in the sight of the Lord our God, for seven days plus seven days, that is, fourteen days.
Ta haka Solomon da dukan Isra’ila, wato, babban taro, suka yi bikin a lokacin. Mutane suka zo, tun daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar. Suka yi biki a gaban Ubangiji Allahnmu, kwana bakwai. Suka kuma ƙara kwana bakwai, kwanaki goma sha huɗu gaba ɗaya.
66 And on the eighth day, he dismissed the people. And blessing the king, they set out for their tents, rejoicing and cheerful in heart over all the good things that the Lord had done for his servant David and for his people Israel.
A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.

< 1 Kings 8 >