< 1 Kings 16 >

1 Then the word of the Lord came to Jehu, the son of Hanani, against Baasha, saying:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Yehu ɗan Hanani game da Ba’asha,
2 “Even though I exalted you from the dust, and I set you as ruler over my people Israel, still you have walked in the way of Jeroboam, and you have caused my people Israel to sin, so that you have provoked me by their sins.
“Na ɗaga ka daga ƙura na mai da kai shugaban mutanena Isra’ila, amma ka yi tafiya a hanyoyin Yerobowam, ka kuma sa mutanena Isra’ila suka yi zunubi, ka tsokane ni na yi fushi ta wurin zunubansu.
3 Behold, I will cut down the posterity of Baasha, and the posterity of his house. And I will make your house like the house of Jeroboam, the son of Nebat.
Saboda haka ina gab da cinye Ba’asha da gidansa, zan kuma mai da gidanka kamar na Yerobowam ɗan Nebat.
4 Whoever will have died of Baasha in the city, the dogs will consume him. And whoever will have died of him in the countryside, the birds of the air will consume him.”
Karnuka za su cinye waɗanda suke na Ba’asha da suka mutu a birni, tsuntsaye kuma za su cinye waɗanda suka mutu a jeji.”
5 Now the rest of the words of Baasha, and whatever he did, and his battles, were these not written in the book of the words of the days of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Ba’asha, abin da ya yi, da kuma nasarorinsa, an rubuta su cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
6 Then Baasha slept with his fathers, and he was buried at Tirzah. And Elah, his son, reigned in his place.
Ba’asha ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Tirza. Sai Ela ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
7 And when the word of the Lord had arrived by the hand of the prophet Jehu, the son of Hanani, against Baasha, and against his house, and against every evil that he had done before the Lord, so that he provoked him by the works of his hands, so that he became like the house of Jeroboam: for this reason, he killed him, that is, the prophet Jehu, the son of Hanani.
Ban da haka, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Yehu ɗan Hanani wa Ba’asha da gidansa, saboda dukan muguntar da ya aikata a gaban Ubangiji, ya tsokane shi yă yi fushi ta wurin abubuwan da ya yi, da kuma zama kamar gidan Yerobowam, da kuma domin ya hallaka gidan Yerobowam.
8 In the twenty-sixth year of Asa, the king of Judah, Elah, the son of Baasha, reigned over Israel, at Tirzah, for two years.
A shekara ta ashirin da shida ta Asa sarkin Yahuda, Ela ɗan Ba’asha ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi mulki a Tirza shekaru biyu.
9 And his servant Zimri, the commander of one half part of the horsemen, rebelled against him. Now Elah was drinking at Tirzah, and he became inebriated in the house of Arza, the prefect of Tirzah.
Zimri, ɗaya daga cikin shugabanni, wanda ya shugabanci rabin kekunan yaƙin Ela, ya yi maƙarƙashiya a kansa. Ela yana a Tirza a lokacin, ya bugu a gidan Arza, sarkin fada a Tirza.
10 Then Zimri, rushing in, struck him and killed him, in the twenty-seventh year of Asa, the king of Judah. And he reigned in his place.
Zimri ya shiga, ya buge shi ya kashe a shekara ta ashirin da bakwai na Asa sarkin Yahuda. Sa’an nan ya gāje shi a matsayin sarki.
11 And when he had reigned and had sat upon his throne, he struck down the entire house of Baasha. And he did not leave behind of them anything that urinates against a wall, among both close relatives and his friends.
Nan da nan sai ya fara mulki ya kuwa zauna a kujerar sarauta, ya kashe dukan iyalin Ba’asha. Bai bar namiji guda ɗaya ba, ko dangi, ko aboki.
12 And so, Zimri destroyed the entire house of Baasha, in accord with the word of the Lord, which he had spoken to Baasha, by the hand the prophet of Jehu,
Ta haka Zimri ya hallaka dukan iyalin Ba’asha, bisa ga maganar da Ubangiji ya yi game da Ba’asha ta wurin annabi Yehu.
13 because of all the sins of Baasha, and the sins of Elah, his son, who sinned and caused Israel to sin, provoking the Lord, the God of Israel, with their vanities.
Wannan ya faru saboda dukan zunuban Ba’asha da waɗanda ɗansa Ela ya yi, da ya sa Isra’ila suka yi, har suka tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, yă yi fushi ta wurin gumakansu marasa amfani.
14 But the rest of the words of Elah, and all that he did, were these not written in the book of the words of the days of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Ela, da dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
15 In the twenty-seventh year of Asa, the king of Judah, Zimri reigned for seven days in Tirzah. For the army was besieging Gibbethon, a city of the Philistines.
A shekara ta ashirin da bakwai na Asa sarkin Yahuda, Zimri ya yi mulki a Tirza kwana bakwai. Mayaƙa suka yi sansani kusa da Gibbeton, wani garin Filistiyawa.
16 And when they had heard that Zimri had rebelled, and that he had killed the king, all of Israel made Omri as a king for themselves; he was the leader of the military over Israel in the encampment in that day.
Sa’ad da Isra’ilawa a cikin sansani suka ji cewa Zimri ya yi maƙarƙashiya a kan sarki, ya kuma kashe shi, sai suka yi shela, suka naɗa Omri, shugaban mayaƙa ya zama sarki a bisa Isra’ila, a wannan rana a cikin sansani.
17 Therefore, Omri ascended, and all of Israel with him, from Gibbethon, and they besieged Tirzah.
Sai Omri da dukan Isra’ilawa suka janye daga Gibbeton, suka yi wa Tirza kwanto.
18 Then Zimri, seeing that the city was about to be taken, entered the palace, and he set fire to himself along with the royal house. And he died
Da Zimri ya ga cewa an kame birnin, sai ya je ya shiga hasumiya fadan sarki ya sa wa fadan wuta wutar kuwa ta ƙone shi ya mutu.
19 in his sins, which he had sinned, doing evil before the Lord, and walking in the way of Jeroboam, and in his sin, by which he caused Israel to sin.
Wannan ya faru saboda zunuban da ya yi, ya yi mugunta a gaban Ubangiji ya kuma yi tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubin da Yerobowam ya yi da ya sa Isra’ila suka yi.
20 But the rest of the words of Zimri, and of his treachery and tyranny, were these not written in the book of the words of the days of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Zimri, da tawayen da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
21 Then the people of Israel were divided into two parts: one half part of the people followed Tibni, the son of Ginath, having appointed him as king, and one half part followed Omri.
Sai mutanen Isra’ila suka rabu kashi biyu; rabi guda sun goyi bayan Tibni ɗan Ginat yă zama sarki, ɗayan rabin kuma sun goyi bayan Omri.
22 But the people who were with Omri prevailed over the people who were following Tibni, the son of Ginath. And Tibni died, and Omri reigned.
Amma mabiyan Omri suka nuna sun fi na Tibni ɗan Ginat ƙarfi. Sai Tibni ya mutu, Omri kuwa ya zama sarki.
23 In the thirty-first year of Asa, the king of Judah, Omri reigned over Israel for twelve years; he reigned for six years at Tirzah.
A shekara ta talatin da ɗaya na Asa sarkin Yahuda, Omri ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu, shekaru shida a Tirza.
24 And he bought the mount of Samaria from Shemer for two talents of silver. And he built upon it, and he called the name of the city that he had built, Samaria, after the name of Shemer, the owner of the mount.
Ya saya tudun Samariya daga Shemer, a bakin talentin biyu na azurfa, ya kuma gina birni a kan tudun, ya kira shi Samariya, bayan Shemer, sunan mai tudun a dā.
25 But Omri did evil in the sight of the Lord, and he wrought wickedness, beyond all who had been before him.
Amma Omri ya yi mugunta a gaban Ubangiji, ya kuma yi zunubi fiye da dukan waɗanda suka kasance kafin shi.
26 And he walked in all the ways of Jeroboam, the son of Nebat, and in his sins, by which he had caused Israel to sin, so that he provoked the Lord, the God of Israel, by their vanities.
Ya yi tafiya a dukan hanyoyin Yerobowam ɗan Nebat da kuma cikin zunubinsa wanda ya sa Isra’ila suka yi, har suka tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila yă yi fushi ta wurin gumakansu marasa amfani.
27 Now the rest of the words of Omri, and his battles that he carried out, were these not written in the book of the words of the days of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Omri, abin da ya yi, da kuma abubuwan da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
28 And Omri slept with his fathers, and he was buried in Samaria. And Ahab, his son, reigned in his place.
Omri ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Samariya. Sai Ahab ya gāje shi a matsayin sarki.
29 Truly, Ahab, the son of Omri, reigned over Israel in the thirty-eighth year of Asa, the king of Judah. And Ahab, the son of Omri, reigned over Israel at Samaria for twenty-two years.
A shekara ta talatin da takwas ta Asa sarkin Yahuda, Ahab ɗan Omri ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi mulki a Samariya a kan Isra’ila, shekara ashirin da biyu.
30 And Ahab, the son of Omri, did evil in the sight of the Lord, beyond all who had been before him.
Ahab ɗan Omri ya yi mugunta sosai a gaban Ubangiji fiye da wani daga cikin waɗanda suka riga shi.
31 And it was not enough for him to walk in the sins of Jeroboam, the son of Nebat. In addition, he took as a wife Jezebel, the daughter of Eth-baal, the king of the Sidonians. And he went astray, and he served Baal, and adored him.
Bai zama masa wani abu mai wuya ba, yă yi zunuban Yerobowam ɗan Nebat, har ma ya auri Yezebel’yar Etba’al sarkin Sidoniyawa, ya kuma fara bauta wa Ba’al, ya yi masa sujada.
32 And he set up an altar for Baal, in the temple of Baal, which he had built at Samaria.
Ya kafa bagade domin Ba’al a haikalin Ba’al da ya gina a Samariya.
33 And he planted a sacred grove. And Ahab added to his works, provoking the Lord, the God of Israel, beyond all the kings of Israel who had been before him.
Ahab ya gina ginshiƙin Ashera, ya kuma aikata abubuwa masu yawa don yă tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila yă yi fushi fiye da dukan sarakunan Isra’ila da suka riga shi.
34 In his days, Hiel from Bethel built up Jericho. With Abiram, his firstborn, he founded it, and with Segub, his youngest son, he set up its gates, in accord with the word of the Lord, which he had spoken by the hand of Joshua, the son of Nun.
A lokaci Ahab ne, Hiyel mutumin Betel ya sāke gina Yeriko. Ya kafa tushensa a bakin ran ɗan farinsa Abiram, ya kuma kafa ƙofofinsa a bakin ran autansa Segub, bisa ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Yoshuwa ɗan Nun.

< 1 Kings 16 >