< 1 Chronicles 9 >

1 And so, all of Israel was numbered. And the sum of them was written in the book of the kings of Israel and of Judah. And they were taken away to Babylon because of their transgression.
Haka aka lissafta dukan Isra’ila a tarihin zuriyoyi a littafin sarakunan Isra’ila. Aka kwasa mutanen Yahuda zuwa zaman bauta a Babilon domin rashin aminci.
2 Now the first who lived in their possessions and in their cities were Israel, and the priests, and the Levites, and the temple servants.
To, na farkon da aka sāke zaunar da su a mallakarsu a garuruwansu, su ne waɗansu Isra’ilawa, firistoci, Lawiyawa da kuma masu hidimar haikali.
3 Staying in Jerusalem were some from the sons of Judah, and from the sons of Benjamin, and also from the sons of Ephraim and of Manasseh:
Waɗanda suke daga Yahuda, daga Benyamin, da kuma daga Efraim da Manasse waɗanda suka zauna a Urushalima su ne,
4 Uthai, the son of Ammihud, the son of Omri, the son of Imri, the son of Bani, from the sons of Perez, the son of Judah.
Uttai ɗan Ammihud, ɗan Omri, ɗan Imri, ɗan Bani, zuriyar Ferez ɗan Yahuda.
5 And from Shiloni: Asaiah the firstborn, and his sons.
Na mutanen Shilo kuwa su ne, Asahiya ɗan fari da’ya’yansa maza.
6 Then from the sons of Zerah: Jeuel, and their brothers, six hundred ninety.
Na mutanen Zera su ne, Yewuyel. Mutane daga Yahuda sun kai 690.
7 And from the sons of Benjamin: Sallu, the son of Meshullam, the son of Hodaviah, the son of Hassenuah;
Na Benyamin su ne, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Hodawiya, ɗan Hassenuwa;
8 and Ibneiah, the son of Jeroham; and Elah, the son of Uzzi, the son of Michri; and Meshullam, the son of Shephatiah, the son of Reuel, the son of Ibnijah;
Ibnehiya ɗan Yeroham; Ela ɗan Uzzi, ɗan Mikri; da Meshullam ɗan Shefatiya, ɗan Reyuwel, ɗan Ibniya.
9 and their brothers according to their families, nine hundred fifty-six. All these were leaders of their kindred, according to the houses of their fathers.
Mutane daga Benyamin, kamar yadda aka lissafta zuriyarsu, sun kai 956. Dukan waɗannan mutane kawunan iyalansu ne.
10 And from the priests: Jedaiah, Jehoiarib, and Jachin;
Na firistoci su ne, Yedahiya; Yehoyarib; Yakin;
11 and also Azariah, the son of Hilkiah, the son of Meshullam, the son of Zadok, the son of Meraioth, the son of Ahitub, the high priest of the house of God;
Azariya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, shugaban da yake lura da gidan Allah;
12 then Adaiah, the son of Jeroham, the son of Pashhur, the son of Malchijah; and Maasai, the son of Adiel, the son of Jahzerah, the son of Meshullam, the son of Meshillemith, the son of Immer;
Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya; da Ma’asai ɗan Adiyel, ɗan Yazera, ɗan Meshullam, ɗan Meshillemit, ɗan Immer.
13 and also their brothers, leaders according to their families, one thousand seven hundred sixty, very strong experienced men, for the work of the ministry in the house of God.
Firistocin da suke kawunan iyalai, sun kai 1,760. Dukansu ƙwararru ne, masu hakkin hidima a cikin gidan Allah.
14 Then from the Levites: Shemaiah, the son of Hasshub, the son of Azrikam, the son of Hashabiah, of the sons of Merari;
Na Lawiyawa su ne, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, mutumin Merari;
15 and also Bakbakkar the carpenter; and Galal; and Mattaniah, the son of Mica, the son of Zichri, the son of Asaph;
Bakbakkar, Heresh, Galal da Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zikri, ɗan Asaf;
16 and Obadiah, the son of Shemaiah, the son of Galal, the son of Jeduthun; and Berechiah, the son of Asa, the son of Elkanah, who lived at the entrance to Netophah.
Obadiya ɗan Shemahiya, ɗan Galal, ɗan Yedutun; da Berekiya ɗan Asa, ɗan Elkana, wanda ya zauna a ƙauyukan Netofawa.
17 Now the gatekeepers were Shallum, and Akkub, and Talmon, and Ahiman; and their brother Shallum was the leader.
Matsaran ƙofofi su ne, Shallum, Akkub, Talmon, Ahiman da’yan’uwansu. Shallum ne babbansu
18 For until that time, at the gate of the king to the east, the sons of Levi served in their turns.
da aka ajiye a Ƙofar Sarki a gabas, har zuwa wannan lokaci. Waɗannan su ne matsaran ƙofofi na sansanin Lawiyawa.
19 Truly, Shallum, the son of Kore, the son of Ebiasaph, the son of Korah, with his brothers and his father’s house, these Korahites, were over the works of the ministry of keeping the vestibules of the tabernacle. And their families, in turns, were keepers of the entrance to the camp of the Lord.
Shallum ɗan Kore, ɗan Ebiyasaf, ɗan Kora, da’yan’uwansa matsaran ƙofofi daga iyalin (mutanen Kohat) su suke da hakkin tsaron madogaran ƙofar Tenti kamar dai yadda kakanninsu suka kasance da hakkin tsaron mashigin mazaunin Ubangiji.
20 Now Phinehas, the son of Eleazar, was their ruler before the Lord.
A dā Finehas ɗan Eleyazar ne yake lura da matsaran, kuma Ubangiji ya kasance tare da shi.
21 But Zechariah, the son of Meshelemiah, was the keeper of the gate of the tabernacle of the testimony.
Zakariya ɗan Meshelemiya shi ne mai tsaro a mashigin Tentin Sujada.
22 All these, chosen as porters for the gates, were two hundred twelve. And they were recorded in their own towns, those whom David, and the seer Samuel, appointed, in their faith,
Duka-duka, waɗanda aka zaɓa don su zama matsaran madogaran ƙofa sun kai 212. Aka rubuta su zuriya-zuriya a ƙauyukansu. Dawuda da Sama’ila mai duba ne suka sa matsaran a wurarensu na aminci.
23 as with them, so also with their sons, at the gates of the house of the Lord and the tabernacle, by their turns.
Su da zuriyarsu, su suke lura da tsaron ƙofofin gidan Ubangiji, gidan da ake kira Tenti.
24 At the four directions, there were gatekeepers, that is, at the east, and at the west, and at the north, and at the south.
Matsaran suna a kusurwoyi huɗu, gabas, yamma, arewa da kudu.
25 Now their brothers were staying in the villages, and they arrived on their Sabbaths, from time to time.
’Yan’uwansu a ƙauyukansu sukan zo lokaci, lokaci su yi ayyukansu kwana bakwai, bakwai.
26 To these four Levites were entrusted the entire number of the gatekeepers, and they were over the chambers and storehouses of the house of the Lord.
Amma manyan matsara huɗu, waɗanda suke Lawiyawa, an danƙa musu hakkin lura da ɗakuna da kuma wuraren ajiya a gidan Allah.
27 And they remained in their watches, on all sides of the temple of the Lord, so that, when the time had arrived, they might open the gates in the morning.
Sukan kwana a kewayen gidan Allah, domin dole su tsare shi; kuma su suke lura da mabuɗi don buɗewa a kowace safiya.
28 Some from their kindred were also over the vessels of the ministry. For the vessels were both carried in and carried out according to number.
Waɗansunsu su ne suke lura da kayayyakin da ake amfani da su a hidimar haikali; sukan ƙirga su sa’ad da ake shigar da su da sa’ad da ake fitar da su.
29 Some of them also were entrusted with the equipment of the sanctuary; they were in charge of the fine wheat flour, and the wine, and the oil, and the frankincense, and the aromatics.
An sa waɗansu su lura da kayayyakin da kuma dukan waɗansu kayan wuri mai tsarki, da kuma gari da ruwan inabi, da mai, turare da kuma kayan yaji.
30 Now the sons of the priests composed the ointments from the aromatics.
Amma waɗansu firistoci ne suke harhaɗa kayan yajin.
31 And Mattithiah, a Levite, the firstborn of Shallum the Korahite, was in charge of those things that were cooked in a frying pan.
Wani Balawe mai suna Mattitiya, ɗan farin Shallum mutumin Kora ne aka danƙa masa hakkin toya burodin miƙawa.
32 Now some of the sons of Kohath, their brothers, were over the bread of the presence, so that they might continually prepare it new for each Sabbath.
Waɗansu’yan’uwansu Kohatawa ne suke lura da shiryawa burodin da ake kaiwa a tebur a kowane Asabbaci.
33 These are the leaders of the singing men, according to the families of the Levites, who were dwelling in the chambers, so that they might carry out their ministry continually, day and night.
Waɗanda suke mawaƙa, kawunan iyalan Lawiyawa, sukan zauna a ɗakunan haikali kuma ba sa yin waɗansu ayyuka domin su suke da hakkin aiki dare da rana.
34 The heads of the Levites, leaders according to their families, abode in Jerusalem.
Dukan waɗannan su ne kawunan iyalan Lawiyawa, manya kamar yadda aka lissafta su a zuriyarsu, kuma suna zama a Urushalima.
35 Now in Gibeon, there lived Jeiel, the father of Gibeon, and the name of his wife was Maacah.
Yehiyel mahaifin Gibeyon ya zauna a Gibeyon. Matarsa ita ce Ma’aka
36 His firstborn son was Abdon, and then Zur, and Kish, and Baal, and Ner, and Nadab,
ɗansa na fari kuwa shi ne Abdon, sai Zur, Kish, Ba’al, Ner, Nadab,
37 as well as Gedor, and Ahio, and Zechariah, and Mikloth.
Gedor, Ahiyo, Zakariya da Miklot.
38 Then Mikloth conceived Shimeam. These lived opposite their brothers in Jerusalem, with their brothers.
Miklot shi ne mahaifin Shimeyam. Su ma sun zauna kusa da danginsu a Urushalima.
39 Now Ner conceived Kish, and Kish conceived Saul. And Saul conceived Jonathan, and Malchishua, and Abinadab, and Eshbaal.
Ner shi mahaifin Kish, Kish mahaifin Shawulu, kuma Shawulu shi ne mahaifin Yonatan, Malki-Shuwa, Abinadab da Esh-Ba’al.
40 And the son of Jonathan was Meribbaal. And Meribbaal conceived Micah.
Ɗan Yonatan shi ne, Merib-Ba’al wanda shi ne mahaifin Mika.
41 Now the sons of Micah were Pithon, and Melech, and Tahrea, and Ahaz.
’Ya’yan Mika maza su ne, Fiton, Melek, Tareya da Ahaz.
42 And Ahaz conceived Jarah. And Jarah conceived Alemeth, and Azmaveth, and Zimri. Then Zimri conceived Moza.
Ahaz shi ne mahaifin Yada, Yada shi ne mahaifin Alemet, Azmawet da Zimri, Zimri kuwa shi ne mahaifin Moza.
43 Truly, Moza conceived Binea, whose son, Rephaiah, conceived Eleasah, from of whom was born Azel.
Moza shi ne mahaifin Bineya; Refahiya, Eleyasa da kuma Azel.
44 Now Azel had six sons, whose names are: Azrikam, Bocheru, Ishmael, Sheariah, Obadiah, Hanan. These are the sons of Azel.
Azel yana da’ya’ya maza shida, kuma ga sunayensu. Azrikam, Bokeru, Ishmayel, Sheyariya, Obadiya da Hanan. Waɗannan su ne’ya’yan Azel maza.

< 1 Chronicles 9 >