< 1 Chronicles 25 >

1 Then David and the magistrates of the army set apart, for the ministry, the sons of Asaph, and of Heman, and of Jeduthun, who were to prophesy with harps and psalteries and cymbals, in accord with their number, having been dedicated to their appointed office.
Dawuda tare da shugabannin mayaƙa, suka keɓe waɗansu daga’ya’yan Asaf, Heman da Yedutun don hidimar yin annabci, suna amfani da garayu, molaye da ganguna. Ga jerin mutanen da suka yi wannan hidima.
2 From the sons of Asaph: Zaccur, and Joseph, and Nethaniah, and Asharelah, the sons of Asaph, under the hand of Asaph, prophesying beside the king.
Daga’ya’yan Asaf, Zakkur, Yusuf, Netaniya da Asarela.’Ya’yan Asaf sun kasance a ƙarƙashin kulawar Asaf, wanda ya yi annabci a ƙarƙashin kulawar sarki.
3 Then of Jeduthun, the sons of Jeduthun: Gedaliah, Zeri, Jeshaiah, and Hashabiah, and Mattithiah, six, under the hand of their father Jeduthun, who was prophesying with stringed instruments, while confessing and praising the Lord.
Game da Yedutun kuwa, daga’ya’yansa maza. Gedaliya, Zeri, Yeshahiya, Shimeyi, Hashabiya da Mattitiya, su shida ne duka, a ƙarƙashin kulawar mahaifinsu Yedutun, wanda ya yi annabci, yana amfani da garaya a yin godiya da yabon Ubangiji.
4 Also, of Heman, the sons of Heman: Bukkiah, Mattaniah, Uzziel, Shebuel, and Jerimoth, Hananiah, Hanani, Eliathah, Giddalti, and Romamtiezer, and Joshbekashah, Mallothi, Hothir, Mahazioth.
Game da Heman kuwa, daga’ya’yansa maza. Bukkiya, Mattaniya, Uzziyel, Shebuwel, Yerimot; Hananiya, Hanani, Eliyata, Giddalti, Romamti-Ezer, Yoshbekasha, Malloti, Hotir da Mahaziyot.
5 All these were the sons of Heman, the seer of the king in the words of God, in order to lift up the horn. And God gave to Heman fourteen sons and three daughters.
Dukan waɗannan’ya’yan Heman ne mai duba na sarki. An ba shi su ta wurin alkawarin Allah don yă ɗaukaka shi. Allah ya ba Heman’ya’ya maza goma sha huɗu da’ya’ya mata uku.
6 All these, under their father’s hand, were distributed in order to sing in the temple of the Lord, with cymbals and psalteries and harps, in the ministry of the house of the Lord beside the king, specifically, Asaph, and Jeduthun, and Heman.
Dukan waɗannan mutane suna a ƙarƙashin kulawar mahaifansu don kaɗe-kaɗe da bushe-bushe a cikin haikalin Ubangiji, da ganguna, molaye da garayu, don hidima a gidan Allah. Asaf, Yedutun da Heman suna ƙarƙashin kulawar sarki.
7 Now the number of these, with their brothers, who were instructing in the song of the Lord, all the teachers, were two hundred eighty-eight.
Da su da danginsu, dukansu su 288 ne kuma horarru da ƙwararru ne a kaɗe-kaɗe da bushe-bushe domin Ubangiji.
8 And they cast lots in their turns, the elder equally with the younger, the learned together with the unlearned.
Baba ko yaro, malami ko ɗalibi, duk suka jefa ƙuri’a saboda ayyukan da za su yi.
9 And the first lot went forth to Joseph, who was of Asaph; the second went forth to Gedaliah, to him and his sons and his brothers, twelve.
Ƙuri’a ta fari, wadda take don Asaf, ta fāɗo a kan Yusuf,’ya’yansa maza da danginsa, 12 ta biyu a kan Gedaliya, danginsa da’ya’yansa maza, 12
10 The third went to Zaccur, to his sons and brothers, twelve.
ta uku a kan Zakkur,’ya’yansa da danginsa, 12
11 The fourth went to Izri, to his sons and brothers, twelve.
ta huɗu a kan Izri,’ya’yansa maza da danginsa, 12
12 The fifth went to Nethaniah, to his sons and brothers, twelve.
ta biyar a kan Netaniya,’ya’yansa maza da danginsa, 12
13 The sixth went to Bukkiah, to his sons and brothers, twelve.
ta shida a kan Bukkiya,’ya’yansa maza da danginsa, 12
14 The seventh went to Jesharelah, to his sons and brothers, twelve.
ta bakwai a kan Yesarela,’ya’yansa maza da danginsa, 12
15 The eighth went to Jeshaiah, to his sons and brothers, twelve.
ta takwas a kan Yeshahiya,’ya’yansa maza da danginsa, 12
16 The ninth went to Mattaniah, to his sons and brothers, twelve.
ta tara a kan Mattaniya,’ya’yansa maza da danginsa, 12
17 The tenth went to Shimei, to his sons and brothers, twelve.
ta goma a kan Shimeyi,’ya’yansa maza da danginsa, 12
18 The eleventh went to Azarel, to his sons and brothers, twelve.
ta goma sha ɗaya a kan Azarel,’ya’yansa maza da danginsa, 12
19 The twelfth went to Hashabiah, to his sons and brothers, twelve.
ta goma sha biyu a kan Hashabiya,’ya’yansa maza da danginsa, 12
20 The thirteenth went to Shubael, to his sons and brothers, twelve.
ta goma sha uku a kan Shubayel,’ya’yansa maza da danginsa, 12
21 The fourteenth went to Mattithiah, to his sons and brothers, twelve.
ta goma sha huɗu a kan Mattitiya,’ya’yansa maza da danginsa, 12
22 The fifteenth went to Jeremoth, to his sons and brothers, twelve.
ta goma sha biya a kan Yeremot,’ya’yansa maza da danginsa, 12
23 The sixteenth went to Hananiah, to his sons and brothers, twelve.
ta goma sha shida a kan Hananiya, na goma sha biya a kan Yerimot,’ya’yansa maza da danginsa, 12
24 The seventeenth went to Joshbekashah, to his sons and brothers, twelve.
ta goma sha bakwai a kan Yoshbekasha, na goma sha biya a kan Yerimot,’ya’yansa maza da danginsa, 12
25 The eighteenth went to Hanani, to his sons and brothers, twelve.
ta goma sha takwas a kan Hanani, na goma sha biya a kan Yerimot,’ya’yansa maza da danginsa 12
26 The nineteenth went to Mallothi, to his sons and his brothers, twelve.
ta goma sha tara a kan Malloti, na goma sha biya a kan Yerimot,’ya’yansa maza da danginsa, 12
27 The twentieth went to Eliathah, to his sons and brothers, twelve.
ta ashirin a kan Eliyata, na goma sha biya a kan Yerimot,’ya’yansa maza da danginsa, 12
28 The twenty-first went to Hothir, to his sons and brothers, twelve.
ta ashirin da ɗaya a kan Hotir, na goma sha biya a kan Yerimot,’ya’yansa maza da danginsa, 12
29 The twenty-second went to Giddalti, to his sons and brothers, twelve.
ta ashirin da biyu a kan Giddalti, na goma sha biya a kan Yerimot,’ya’yansa maza da danginsa, 12
30 The twenty-third went to Mahazioth, to his sons and brothers, twelve.
ta ashirin da uku a kan Mahaziyot, na goma sha biya a kan Yerimot,’ya’yansa maza da danginsa, 12
31 The twenty-fourth went to Romamtiezer, to his sons and brothers, twelve.
ta ashirin da huɗu a kan Romamti-Ezer, na goma sha biya a kan Yerimot,’ya’yansa maza da danginsa 12.

< 1 Chronicles 25 >