< Ruth 4 >

1 And Booz went up to the gate, and sat there; and behold, the relative passed by, of whom Booz spoke: and Booz said to him, Turn aside, sit down here, such a one: and he turned aside and sat down.
Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
2 And Booz took ten men of the elders of the city, and said, Sit you here; and they sat down.
Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
3 And Booz said to the relative, [The matter regards] the portion of the field which was our brother Elimelech's which was given to Noemin, now returning out of the land of Moab;
Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
4 and I said, I will inform you, saying, Buy it before those that sit, and before the elders of my people: if you will redeem it, redeem it, but if you will not redeem it, tell me, and I shall know; for there is no one beside you to do the office of a kinsman, and I am after you: and he said, I am [here], I will redeem it.
Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
5 And Booz said, In the day of your buying the field of the hand of Noemin and of Ruth the Moabitess the wife of the deceased, you must also buy her, so as to raise up the name of the dead upon his inheritance.
Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
6 And the kinsman said, I shall not be able to redeem it for myself, lest I mar my own inheritance; do you redeem my right for yourself, for I shall not be able to redeem [it].
Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
7 And this [was] in former time the ordinance in Israel for redemption, and for a bargain, to confirm every word: A man loosed his shoe, and gave it to his neighbour that redeemed his right; and this was a testimony in Israel.
(To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
8 And the kinsman said to Booz, Buy my right for yourself: and he took off his shoe and gave it to him.
Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
9 And Booz said to the elders and to all the people, You [are] this day witnesses, that I have bought all that was Elimelech's, and all that belonged to Chelaion and Maalon, of the hand of Noemin.
Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
10 Moreover I have bought for myself for a wife Ruth the Moabitess, the wife of Maalon, to raise up the name of the dead upon his inheritance; so the name of the dead shall not be destroyed from amongst his brethren, and from the tribe of his people: you [are] this day witnesses.
Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
11 And all the people who were in the gate said, [We are] witnesses: and the elders said, The Lord make your wife who goes into your house, as Rachel and as Lia, who both [together] built the house of Israel, and wrought mightily in Ephratha, and there shall be a name [to you] in Bethleem.
Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
12 And let your house be as the house of Phares, whom Thamar bore to Juda, of the seed which the Lord shall give you of this handmaid.
Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
13 And Booz took Ruth, and she became his wife, and he went in to her; and the Lord gave her conception, and she bore a son.
Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
14 And the woman said to Noemin, Blessed [is] the Lord, who has not suffered a redeemer to fail you this day, even to make your name famous in Israel.
Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
15 And he shall be to you a restorer of your soul, and one to cherish your old age; for your daughter-in-law which has loved you, who is better to you than seven sons, has born him.
Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
16 And Noemin took the child and laid it in her bosom, and became a nurse to it.
Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
17 And the neighbours gave it a name, saying, A son has been born to Noemin; and they called his name Obed; this [is] the father of Jessae the father of David.
Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
18 And these [are] the generations of Phares: Phares begot Esrom:
Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
19 Esrom begot Aram; and Aram begot Aminadab.
Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
20 And Aminadab begot Naasson; and Naasson begot Salmon.
Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
21 And Salmon begot Booz; and Booz begot Obed.
Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
22 And Obed begot Jessae; and Jessae begot David.
Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.

< Ruth 4 >