< Psalms 36 >

1 For the end, by David the servant of the Lord. The transgressor, that he may sin, says within himself, [that] there is no fear of God before his eyes.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Akwai magana a cikin zuciyata game da zunubin mugu. Babu tsoron Allah a idanunsa.
2 For he has dealt craftily before him, to discover his iniquity and hate it.
Gama a idanunsa yana ganin kansa wani abu ne wanda ya sha ƙarfi a gane ko ya ƙi zunubinsa.
3 The words of his mouth are transgression and deceit: he is not inclined to understand [how] to do good.
Kalmomin bakinsa mugaye ne da kuma ruɗu; ya daina zama mai hikima da yin alheri.
4 He devises iniquity on his bed; he gives himself to every evil way; and does not abhor evil.
Ko a kan gadonsa ma yana shirya mugunta; yakan sa kansa ga aikata zunubi kuma ba ya ƙin abin da ba shi da kyau.
5 O Lord, your mercy is in the heaven; and your truth [reaches] to the clouds.
Ƙaunarka, ya Ubangiji, kan kai sammai, amincinka har sararin sammai.
6 Your righteousness is as the mountains of God, your judgements are as a great deep: O Lord, you will preserve men and beasts.
Adalcinka yana kama da manyan duwatsu, hukuncinka kamar zurfi mai girma. Ya Ubangiji, kana lura da mutum da dabba.
7 How have you multiplied your mercy, O God! so the children of men shall trust in the shelter of your wings.
Ina misalin ƙaunarka marar ƙarewa! Mutane manya da ƙanana kan sami mafaka cikin inuwar fikafikanka.
8 They shall be fully satisfied with the fatness of your house; and you shall cause them to drink of the full stream of your delights.
Suna biki a yalwar gidanka; kakan ba su sha daga rafin farin cikinka.
9 For with you is the fountain of life: in your light we shall see light.
Gama a gare ka akwai maɓulɓular rai cikin haskenka mukan ga haske.
10 Extend your mercy to them that know you; and your righteousness to the upright in heart.
Ka ci gaba da ƙaunarka ga waɗanda suka san ka, adalcinka ga masu gaskiyar zuciya.
11 Let not the foot of pride come against me, and let not the hand of sinners move me.
Kada ka bari ƙafar mai girman kai yă fāɗa mini, ko hannun mugu ya kore ni.
12 There have all the workers of iniquity fallen: they are cast out, and shall not be able to stand.
Dubi yadda masu aikata zunubi suka fāɗi, a zube, ba za su kuwa iya tashi ba!

< Psalms 36 >