< Chronicles II 25 >

1 Amasias began to reign when he was twenty and five years old, and he reigned twenty-nine years in Jerusalem; and his mother's name [was] Joadaen of Jerusalem.
Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin ce; ita daga Urushalima ne.
2 And he did that which was right in the sight of the Lord, but not with a perfect heart.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma ba da dukan zuciyarsa ba.
3 And it came to pass, when the kingdom was established in his hand, that he killed his servants who had slain the king his father.
Bayan sarauta ta kahu a ƙarƙashinsa, sai ya kashe hafsoshin da suka kashe mahaifinsa sarki.
4 But he killed not their sons, according to the covenant of the law of the Lord, as it is written, [and] as the Lord commanded, saying, The fathers shall not die for the children, and the sons shall not die for the fathers, but they shall die each for his own sin.
Duk da haka bai kashe’ya’yansu maza ba amma ya yi bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Doka, a cikin Littafin Musa, inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda’ya’yansu ba; ba kuwa za a kashe’ya’ya saboda iyayensu ba; kowa zai mutu saboda zunubansa ne.”
5 And Amasias assembled the house of Juda, and appointed them according to the houses of their families for captains of thousands and captains of hundreds in all Juda and Jerusalem: and he numbered them from twenty years old and upwards, and found them three hundred thousand able to go out to war, holding spear and shield.
Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya kuma ba su aiki bisa ga iyalansu, ya ba da aiki ga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, a dukan Yahuda da Benyamin. Ya kuma tattara waɗanda suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye ya sami mutane dubu ɗari uku da suke a shirye don aikin soja, da suka isa riƙe māshi da garkuwa.
6 Also he hired of Israel a hundred thousand mighty [men for] a hundred talents of silver.
Ya kuma ɗauko sojan haya jarumawa dubu ɗari ɗaya daga Isra’ila a kan talenti ɗari na azurfa.
7 And there came a man of God to him, saying, O king, let not the host of Israel go with you; for the Lord is not with Israel, [even] all the sons of Ephraim.
Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, waɗannan runduna daga Isra’ila ba za su tafi tare da kai ba, gama Ubangiji ba ya tare da Isra’ila, ba ya nan da wani cikin mutanen Efraim.
8 For if you shall undertake to strengthen [yourself] with these, then the lord shall put you to flight before the enemies: for it is of the Lord both to strengthen and to put to flight.
Ko da ma ya tafi ya yi faɗa da ƙwazo a cikin yaƙi, Allah zai tumɓuke shi a gaban abokan gāba, gama Allah yana da iko yă taimaka ko yă tumɓuke.”
9 And Amasias said to the man of God, But what shall I do [for] the hundred talents which I have given to the army of Israel? And the man of God said, The Lord can give you much more than these.
Amaziya ya tambayi mutumin Allah ya ce, “Amma game da talenti ɗarin da na biya saboda waɗannan rundunonin Isra’ila fa?” Mutumin Allah ya amsa, “Ubangiji zai ba ka fiye da wannan.”
10 And Amasias separated from the army that came to him from Ephraim, that they might go away to their place; and they were very angry with Juda, and they returned to their place with great wrath.
Saboda haka Amaziya ya sallame rundunonin da suka zo daga Efraim, ya kuma mayar da su gida. Suka husata da Yahuda suka koma gida da fushi sosai.
11 And Amasias strengthened [himself], and took his people, and went to the valley of salt, and struck there the children of Seir ten thousand.
Sa’an nan Amaziya ya yi ƙarfin hali ya jagoranci mayaƙansa zuwa Kwarin Gishiri, inda ya kashe mutanen Seyir dubu goma.
12 And the children of Juda took ten thousand prisoners, and they carried them to the top of the precipice, and cast them headlong from the top of the precipice, and they were all dashed to pieces.
Mayaƙan Yahuda suka kuma kama mutane dubu goma da rai, suka ɗauke su zuwa ƙwanƙolin dutsen, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa suka yi kaca-kaca.
13 And the men of the host whom Amasias sent back so that they should not go with him to battle, [went] and attacked the cities of Juda, from Samaria to Baethoron; and they struck three thousand amongst them, and took much spoil.
Ana cikin haka, sai rundunar da Amaziya ya mai da su gida, waɗanda ba a bari suka tafi yaƙin ba, suka kai wa garuruwan Yahuda daga Samariya zuwa Bet-Horon hari. Suka kashe mutane dubu uku suka kwashe ganima mai yawan gaske.
14 And it came to pass, after Amasias had returned from striking Idumea, that he brought home the gods of the children of Seir, and set them up for himself as gods, and bowed down before them, and he sacrificed to them.
Da Amaziya ya dawo daga kisan mutanen Edom, sai ya dawo da allolin mutanen Seyir. Ya kafa su a matsayin allolinsa, ya rusuna musu, ya kuma miƙa musu hadayun ƙonawa.
15 And the anger of the Lord came upon Amasias, and he sent him a prophet, and he said to him, Why have you sought the gods of the people, which have not rescued their own people out of your hand?
Fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan Amaziya, sai ya aiki wani annabi wurinsa wanda ya ce, “Me ya sa ka nemi shawarar allolin mutanen nan, waɗanda ba za su cece mutanensu daga hannunka ba?”
16 And it came to pass when the prophet was speaking to him, that he said to him, have I made you king's counsellor? take heed lest you be scourged: and the prophet forebore, and said, I know that [God] is disposed against you to destroy you, because you have done this thing, and have not listened to my counsel.
Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
17 And Amasias king of Juda took counsel, and sent to Joas, son of Joachaz, son of Jeu, king of Israel, saying, Come, and let us look one another in the face.
Bayan Amaziya sarkin Yahuda ya nemi shawara mashawartansa, sai ya kalubalanci Yowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, “Zo mu gamu fuska da fuska.”
18 And Joas king of Israel sent to Amasias king of Juda, saying, The thistle that was in Libanus sent to the cedar that was in Libanus, saying, Give your daughter to my son to wife; but, behold, your wild beasts of the field that are in Libanus shall come: and the wild beasts did come, and trod down the thistle.
Amma Yowash sarkin Isra’ila ya amsa wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika da saƙo wa itacen al’ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Sai wani naman jeji na Lebanon ya zo ya tattake ƙayar.
19 You have said, Behold, I have struck Idumea, and your stout heart exalts you: now stay at home; for why do you implicate yourself in mischief, that you should fall, and Juda with you.
Ka ce wa kanka cewa ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana fariya da ɗaga kai. Amma tsaya dai a gida! Me ya sa kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da ta Yahuda?”
20 Nevertheless Amasias listened not, for it was of the Lord to deliver him into [the enemy's] hands, because he sought after the gods of the Idumeans.
Amma Amaziya bai saurara ba gama Allah ya yi haka domin yă miƙa su ga Yehowash, domin sun nemi shawarar allolin Edom.
21 So Joas king of Israel went up; and they saw one another, he and Amasias king of Juda, in Baethsamys, which is of Juda.
Saboda haka Yowash sarkin Isra’ila ya kai yaƙi. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh a Yahuda.
22 And Juda was put to flight before Israel, and they fled every man to his tent.
Isra’ila ta fatattaki Yahuda, sai kowane mutum ya gudu zuwa gidansa.
23 And Joas king of Israel took prisoner Amasias king of Juda, [son] of Joas, son of Joachaz, in Baethsamys, and brought him to Jerusalem; and he pulled down [part] of the wall of Jerusalem from the gate of Ephraim to the corner gate, four hundred cubits.
Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
24 And [he took] all the gold and the silver, and all the vessels that were found in the house of the Lord and with Abdedom, and the treasures of the king's house, and the hostages, and he returned to Samaria.
Ya kwashe dukan zinariya da azurfa da dukan kayayyakin da aka samu a haikalin Allah waɗanda suke a ƙarƙashin kulawar Obed-Edom, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya.
25 And Amasias the [son] of Joas king of Juda lived after the death of Joas the [son] of Joachaz king of Israel fifteen years.
Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya rayu shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
26 And the rest of the acts of Amasias, the first and the last, Behold! are they not written in the book of the kings of Juda and Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
27 And at the time when Amasias departed from the Lord, then they formed a conspiracy against him; and he fled from Jerusalem to Lachis: and they sent after him to Lachis, and killed him there.
Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
28 And they took him up on horses, and buried him with his fathers in the city of David.
Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.

< Chronicles II 25 >