< Psalms 130 >

1 A Song of the going up. Out of the deep have I sent up my cry to you, O Lord.
Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
2 Lord, let my voice come before you: let your ears be awake to the voice of my prayer.
Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
3 O Jah, if you took note of every sin, who would go free?
In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
4 But there is forgiveness with you, so that you may be feared.
Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
5 I am waiting for the Lord, my soul is waiting for him, and my hope is in his word.
Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
6 My soul is watching for the Lord more than those who are watching for the morning; yes, more than the watchers for the morning.
Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
7 O Israel, have hope in the Lord; for with the Lord is mercy and full salvation.
Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
8 And he will make Israel free from all his sins.
Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.

< Psalms 130 >