< Proverbs 2 >

1 My son, if you will take my words to your heart, storing up my laws in your mind;
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2 So that your ear gives attention to wisdom, and your heart is turned to knowledge;
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3 Truly, if you are crying out for good sense, and your request is for knowledge;
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4 If you are looking for her as for silver, and searching for her as for stored-up wealth;
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5 Then the fear of the Lord will be clear to you, and knowledge of God will be yours.
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
6 For the Lord gives wisdom; out of his mouth come knowledge and reason:
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
7 He has salvation stored up for the upright, he is a breastplate to those in whom there is no evil;
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
8 He keeps watch on the ways which are right, and takes care of those who have the fear of him.
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
9 Then you will have knowledge of righteousness and right acting, and upright behaviour, even of every good way.
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
10 For wisdom will come into your heart, and knowledge will be pleasing to your soul;
Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
11 Wise purposes will be watching over you, and knowledge will keep you;
Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
12 Giving you salvation from the evil man, from those whose words are false;
Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
13 Who give up the way of righteousness, to go by dark roads;
waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
14 Who take pleasure in wrongdoing, and have joy in the evil designs of the sinner;
waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
15 Whose ways are not straight, and whose footsteps are turned to evil:
waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
16 To take you out of the power of the strange woman, who says smooth words with her tongue;
Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
17 Who is false to the husband of her early years, and does not keep the agreement of her God in mind:
wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
18 For her house is on the way down to death; her footsteps go down to the shades:
Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
19 Those who go to her do not come back again; their feet do not keep in the ways of life:
Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
20 So that you may go in the way of good men, and keep in the footsteps of the upright.
Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
21 For the upright will be living in the land, and the good will have it for their heritage.
Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
22 But sinners will be cut off from the land, and those whose acts are false will be uprooted.
amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.

< Proverbs 2 >