< Luke 1 >

1 As a number of attempts have been made to put together in order an account of those events which took place among us,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 As they were handed down to us by those who saw them from the first and were preachers of the word,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 It seemed good to me, having made observation, with great care, of the direction of events in their order, to put the facts in writing for you, most noble Theophilus;
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 So that you might have certain knowledge of those things about which you were given teaching.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 In the days of Herod, king of Judaea, there was a certain priest, by name Zacharias, of the order of Abijah; and he had a wife of the family of Aaron, and her name was Elisabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 They were upright in the eyes of God, keeping all the rules and orders of God, and doing no wrong.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 And they were without children, because Elisabeth had never given birth, and they were at that time very old.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Now it came about that in his turn he was acting as priest before God,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 And as was the way of the priests, he had to go into the Temple to see to the burning of perfumes.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 And all the people were offering prayers outside, at the time of the burning of perfumes.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 And he saw an angel of the Lord in his place on the right side of the altar.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 And Zacharias was troubled when he saw him, and fear came on him.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 But the angel said, Have no fear, Zacharias, for your prayer has come to the ears of God, and your wife Elisabeth will have a son, and his name will be John.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 And you will be glad and have great delight; and numbers of people will have joy at his birth.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 For he will be great in the eyes of the Lord; he will not take wine or strong drink; and he will be full of the Spirit of God from his birth.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 And through him great numbers of the children of Israel will be turned to the Lord their God.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 And he will go before his face in the spirit and power of Elijah, turning the hearts of fathers to their children, and wrongdoers to the way of righteousness; to make ready a people whose hearts have been turned to the Lord.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 And Zacharias said to the angel, How may I be certain of this? For I am an old man, and my wife is far on in years.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 And the angel, answering, said, I am Gabriel, whose place is before God; I have been sent to say these words to you and to give you this good news.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Now, see, you will be without voice or language till the day when these things come about, because you had not faith in my words, which will have effect at the right time.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 And the people were waiting for Zacharias and were surprised because he was in the Temple for such a long time.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 And when he came out he was not able to say anything, and they saw that he had seen a vision in the Temple; and he was making signs to them without words.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 And when the days of his work in the Temple were ended, he went back to his house.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 After that time, Elisabeth, being certain that she was to become a mother, kept herself from men's eyes for five months, saying,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 The Lord has done this to me, for his eyes were on me, to take away my shame in the eyes of men.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Now in the sixth month the angel Gabriel was sent from God to a town in Galilee, named Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 To a virgin who was to be married to a man named Joseph, of the family of David; and the name of the virgin was Mary.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 And the angel came in to her and said, Peace be with you, to whom special grace has been given; the Lord is with you.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 But she was greatly troubled at his words, and said to herself, What may be the purpose of these words?
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 And the angel said to her, Have no fear, Mary, for you have God's approval.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 And see, you will give birth to a son, and his name will be Jesus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 He will be great, and will be named the Son of the Most High: and the Lord God will give him the kingdom of David, his father:
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 He will have rule over the house of Jacob for ever, and of his kingdom there will be no end. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 And Mary said to the angel, How may this be, because I have had no knowledge of a man?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 And the angel in answer said to her, The Holy Spirit will come on you, and the power of the Most High will come to rest on you, and so that which will come to birth will be named holy, Son of God.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Even now Elisabeth, who is of your family, is to be a mother, though she is old: and this is the sixth month with her who was without children.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 For there is nothing which God is not able to do.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 And Mary said: I am the servant of the Lord; may it be to me as you say. And the angel went away.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Then Mary got up and went quickly into the high lands, to a town of Judah;
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 And went into the house of Zacharias and took Elisabeth in her arms.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 And when the voice of Mary came to the ears of Elisabeth, the baby made a sudden move inside her; then Elisabeth was full of the Holy Spirit,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 And she said with a loud voice: May blessing be on you among women, and a blessing on the child of your body.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 How is it that the mother of my Lord comes to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For, truly, when the sound of your voice came to my ears, the baby in my body made a sudden move for joy.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Happy will she be who had faith that the things which the Lord has said to her will be done.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 And Mary said: My soul gives glory to God;
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 My spirit is glad in God my Saviour.
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 For he has had pity on his servant, though she is poor and lowly placed: and from this hour will all generations give witness to the blessing which has come to me.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 For he who is strong has done great things for me; and holy is his name.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 His mercy is for all generations in whom is the fear of him.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 With his arm he has done acts of power; he has put to flight those who have pride in their hearts.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He has put down kings from their seats, lifting up on high the men of low degree.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Those who had no food he made full of good things; the men of wealth he sent away with nothing in their hands;
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 His help he has given to Israel, his servant, so that he might keep in mind his mercy to Abraham and his seed for ever,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 As he gave his word to our fathers. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 And Mary was with her for about three months and then went back to her house.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Now it was time for Elisabeth to give birth, and she had a son.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 And it came to the ears of her neighbours and relations that the Lord had been very good to her, and they took part in her joy.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 And on the eighth day they came to see to the circumcision of the child, and they would have given him the name of Zacharias, his father's name;
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 But his mother made answer and said, No, his name is John.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 And they said, Not one of your relations has that name.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 And they made signs to his father, to say what name was to be given to him.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 And he sent for writing materials and put down: His name is John; and they were all surprised.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 And straight away his mouth was open and his tongue was free and he gave praise to God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 And fear came on all those who were living round about them: and there was much talk about all these things in all the hill-country of Judaea.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 And all who had word of them kept them in their minds and said, What will this child be? For the hand of the Lord was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 And his father, Zacharias, was full of the Holy Spirit, and with the voice of a prophet said these words:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Praise be to the Lord, the God of Israel, for he has come to his people and made them free,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Lifting up a horn of salvation for us in the house of his servant David,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 (As he said, by the mouth of his holy prophets, from the earliest times, ) (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Salvation from those who are against us, and from the hands of those who have hate for us;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 To do acts of mercy to our fathers and to keep in mind his holy word,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 The oath which he made to Abraham, our father,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 That we, being made free from the fear of those who are against us, might give him worship,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 In righteousness and holy living before him all our days.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And you, child, will be named the prophet of the Most High: you will go before the face of the Lord, to make ready his ways;
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 To give knowledge of salvation to his people, through the forgiveness of sins,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Because of the loving mercies of our God, by which the dawn from heaven has come to us,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 To give light to those in dark places, and in the shade of death, so that our feet may be guided into the way of peace.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And the child became tall, and strong in spirit; and he was living in the waste land till the day when he came before the eyes of Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >