< Isaiah 4 >

1 And in that day seven women will put their hands on one man, saying, There will be no need for you to give us food or clothing, only let us go under your name, so that our shame may be taken away.
A wannan rana mata guda bakwai za su cafke namiji guda su ce, “Ma ciyar da kanmu mu kuma yi wa kanmu sutura; ka dai bari mu ce kai ne mijinmu. Ka ɗauke mana kunyar da za mu sha.”
2 In that day will the young growth of the Lord be beautiful in glory, and the fruit of the earth will be the pride of those who are still living in Israel.
A wannan rana Reshen Ubangiji zai zama kyakkyawa da kuma ɗaukaka, kuma amfanin ƙasar zai zama abin fariya da ɗaukakar waɗanda suka rayu a Isra’ila.
3 And it will come about that the rest of the living in Zion, and of those who have been kept from destruction in Jerusalem, will be named holy, even everyone who has been recorded for life in Jerusalem:
Waɗanda suka rage a Sihiyona, waɗanda suka rage a Urushalima, za a ce da su masu tsarki, wato, dukan waɗanda aka rubuta a cikin masu rai a Urushalima.
4 When Zion has been washed from her sin by the Lord, and Jerusalem made clean from her blood by a judging and a burning wind.
Ubangiji zai wanke duk wani ƙazantar matan Sihiyona; ya tsabtacce jinin da aka zubar daga Urushalima ta wurin ruhun hukunci da yake ƙuna kamar wuta.
5 And over every living-place on Mount Zion, all over all her meetings, the Lord will make a cloud and smoke by day, and the shining of a flaming fire by night, for over all, the glory of the Lord will be a cover and a tent;
Sa’an nan Ubangiji zai sa girgijen hayaƙi da rana da harshen wuta da dare a bisa dukan Dutsen Sihiyona da kuma bisa waɗanda suka tattaru a can; a bisa duka kuwa ɗaukakar za tă zama rumfa.
6 And a shade in the daytime from the heat, and a safe cover from storm and from rain.
Za tă zama rumfa da inuwar da za tă tare zafin rana, da kuma mafaka da wurin ɓuya daga hadari da ruwan sama.

< Isaiah 4 >