< Ezekiel 32 >

1 And it came about in the twelfth year, in the twelfth month, on the first day of the month, that the word of the Lord came to me, saying,
A shekara ta goma sha biyu, a wata na goma sha biyu a rana ta fari, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Son of man, make a song of grief for Pharaoh, king of Egypt, and say to him, Young lion of the nations, destruction has come on you; and you were like a sea-beast in the seas, sending out bursts of water, troubling the waters with your feet, making their streams dirty.
“Ɗan mutum, ka yi makoki a kan Fir’auna sarkin Masar ka faɗa masa. “‘Kai kamar zaki ne a cikin al’ummai; kai kamar dodon ruwa a cikin tekuna kana ɓullowa cikin rafuffukanka, kana gurɓata ruwa da ƙafafunka kana kuma dama rafuffuka.
3 This is what the Lord has said: My net will be stretched out over you, and I will take you up in my fishing-net.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Da taron jama’a masu yawa zan jefa abin kamun kifi a kanka, za su kuwa jawo ka da abin kamun kifi.
4 And I will let you be stretched on the land; I will send you out violently into the open field; I will let all the birds of heaven come to rest on you and will make the beasts of all the earth full of you.
Zan jefar da kai a ƙasa zan jefa ka a fili. Zan sa dukan tsuntsayen sararin sama su zauna a kanka dukan namun jeji na duniya kuma za su ƙosar da kansu a kanka.
5 And I will put your flesh on the mountains, and make the valleys full of your blood.
Zan baza namanka a kan duwatsu in kuma cika kwaruruka da gawarka.
6 And the land will be watered with your blood, and the waterways will be full of you.
Zan jiƙa ƙasar da jininka mai gudu har zuwa duwatsu, magudanan ruwa za su cika da namanka.
7 And when I put out your life, the heaven will be covered and its stars made dark; I will let the sun be covered with a cloud and the moon will not give her light.
Sa’ad da na shafe ka, zan rufe sammai in duhunta taurarinsu; zan rufe rana da girgije, wata kuwa ba zai ba da haskensa ba.
8 All the bright lights of heaven I will make dark over you, and put dark night on your land, says the Lord.
Dukan haskokin sammai za su zama duhu a kanka; zan kawo duhu a kan ƙasarka, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 And the hearts of numbers of peoples will be troubled, when I send your prisoners among the nations, into a country which is strange to you.
Zan dami zukatan mutane masu yawa sa’ad da na kawo maka hallaka a cikin al’ummai, a cikin ƙasashen da ba ka taɓa sani ba.
10 And I will make a number of peoples overcome with wonder at you, and their kings will be full of fear because of you, when my sword is waved before them: they will be shaking every minute, every man fearing for his life, in the day of your fall.
Zan sa mutane da yawa su giggice saboda abin da ya same ka, sarakunansu kuma za su yi rawar jiki saboda kai sa’ad da na kaɗa takobina a gabansu. A ranar fāɗuwarka kowannensu zai yi rawar jiki a kowane lokaci saboda ransa.
11 For this is what the Lord has said: The sword of the king of Babylon will come on you.
“‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Takobin sarkin Babilon zai auko maka.
12 I will let the swords of the strong be the cause of the fall of your people; all of them men to be feared among the nations: and they will make waste the pride of Egypt, and all its people will come to destruction.
Zan sa jama’arka su mutu ta wurin takuban ƙarfafan mutane, masu bantsoro na dukan al’ummai. Za su lalatar da girman kan Masar, su kuma tumɓuke dukan jama’arta.
13 And I will put an end to all her beasts which are by the great waters, and they will never again be troubled by the foot of man or by the feet of beasts.
Zan hallaka dukan dabbobinta da suke kusa da ruwaye masu yawa ƙafar mutum ba zai ƙara damunsa ko kofaton dabba ya gurɓata shi.
14 Then I will make their waters clear and their rivers will be flowing like oil, says the Lord.
Sa’an nan zan sa ruwanta su kwanta in sa rafuffukanta su gudu kamar mai, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 When I make Egypt an unpeopled waste, cutting off from the land all the things in it; when I send punishment on all those living in it, then it will be clear to them that I am the Lord.
Sa’ad da na mai da Masar kufai na kuma raba ƙasar da abin da take cike da shi, sa’ad da na bugi dukan waɗanda suke cikinta, a sa’an nan ne za su san cewa ni ne Ubangiji.’
16 It is a song of grief, and people will give voice to it, the daughters of the nations will give voice to it, even for Egypt and all her people, says the Lord.
“Wannan ne makokin da za a yi mata.’Yan matan al’ummai za su rera shi; gama Masar da dukan jama’arta za su rera shi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
17 And in the twelfth year, on the fifteenth day of the month, the word of the Lord came to me, saying,
A shekara ta goma sha biyu, a rana ta goma sha biyar ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 Son of man, let your voice be loud in sorrow for the people of Egypt and send them down, even you and the daughters of the nations; I will send them down into the lowest parts of the earth, with those who go down into the underworld.
“Ɗan mutum, yi kuka saboda jama’ar Masar ka kuma tura ta da’yan matan manyan al’ummai zuwa ƙarƙashin ƙasa, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
19 Are you more beautiful than any? go down, and take your rest among those without circumcision,
Ka ce, ‘Kin fi sauran tagomashi ne? Ki gangara, ki kwanta cikin marasa kaciya.’
20 Among those who have been put to the sword: they will give a resting-place with them to all their people.
Za su fāɗi cikin waɗanda aka kashe da takobi. Takobin da an zāre; bari a ja ta a tafi tare da dukan jama’arta.
21 The strong among the great ones will say to him from the underworld, Are you more beautiful than any? go down, you and your helpers, and take your rest among those without circumcision, and those who have been put to the sword. (Sheol h7585)
Daga cikin kabari manyan shugabanni za su yi maganar Masar da abokanta su ce, ‘Sun gangara sun kuma kwanta da marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.’ (Sheol h7585)
22 There is Asshur and all her army, round about her last resting-place: all of them put to death by the sword:
“Assuriya tana can tare da dukan sojojinta; an kewaye ta da kaburburan dukan waɗanda aka kashe, dukan waɗanda suka mutu ta wurin takobi.
23 Whose resting-places are in the inmost parts of the underworld, who were a cause of fear in the land of the living.
Kaburburansu suna cikin zurfafan rami kuma sojojinta suna kwance kewaye da kabarinta. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun mutu, an kashe su da takobi.
24 There is Elam and all her people, round about her last resting-place: all of them put to death by the sword, who have gone down without circumcision into the lowest parts of the earth, who were a cause of fear in the land of the living, and are put to shame with those who go down to the underworld:
“Elam tana can, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu sun mutu, an kashe su da takobi. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun gangara wurin marasa kaciya a duniyar da take ƙarƙashi. Suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
25 They have made a bed for her among the dead, and all her people are round about her resting-place: all of them without circumcision, put to death with the sword; for they were a cause of fear in the land of the living, and are put to shame with those who go down to the underworld: they have been given a place among those who have been put to the sword.
An yi mata gado a cikin matattu, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi. Domin tsoronsu ya bazu cikin ƙasar masu rai, suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami; an kwantar da su tare da waɗanda aka kashe.
26 There is Meshech, Tubal, and all her people, round about her last resting-place: all of them without circumcision, put to death by the sword; for they were a cause of fear in the land of the living.
“Meshek da Tubal suna can, tare da dukan jama’arsu kewaye da kaburburansu. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi domin sun haddasa tsoronsu a ƙasar masu rai.
27 And they have been put to rest with the fighting men who came to their end in days long past, who went down to the underworld with their instruments of war, placing their swords under their heads, and their body-covers are over their bones; for their strength was a cause of fear in the land of the living. (Sheol h7585)
Ba sun kwanta tare da sauran jarumawa marasa kaciyan da aka kashe, waɗanda suka gangara kabari tare da makaman yaƙinsu, waɗanda aka yi musu matashin kai da takubansu ba? Hukuncin zunubansu yana a bisa ƙasusuwansu, ko da yake tsoron waɗannan jarumawa ya manne cikin ƙasar masu rai. (Sheol h7585)
28 But you will have your bed among those without circumcision, and will be put to rest with those who have been put to death with the sword.
“Kai kuma, ya Fir’auna, za a kakkarye ka za ka kuma kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.
29 There is Edom, her kings and all her princes, who have been given a resting-place with those who were put to the sword: they will be resting among those without circumcision, even with those who go down to the underworld.
“Edom tana can, sarakunanta da dukan yerimanta; duk da ikonsu, sun kwanta tare da waɗanda aka kashe da takobi. Suna kwance tare da marasa kaciya, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
30 There are the chiefs of the north, all of them, and all the Zidonians, who have gone down with those who have been put to the sword: they are shamed on account of all the fear caused by their strength; they are resting there without circumcision, among those who have been put to the sword, and are put to shame with those who go down to the underworld.
“Dukan yerima arewa da dukan Sidoniyawa suna can; sun gangara tare da waɗanda aka kashe cikin kunya duk da tsoron da suka haddasa ta wurin ikonsu. Sun kwanta tare da marasa kaciya tare da waɗanda aka kashe da takobi suna kuma shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
31 Pharaoh will see them and be comforted on account of all his people: even Pharaoh and all his army, put to death by the sword, says the Lord.
“Fir’auna, shi da dukan sojojinsa, za su gan su zai kuma ta’azantu domin dukan jama’arsa da aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
32 For he put his fear in the land of the living: and he will be put to rest among those without circumcision, with those who have been put to death with the sword, even Pharaoh and all his people, says the Lord.
Ko da yake na sa ta haddasa tsoro a ƙasar masu rai, Fir’auna da dukan jama’arsa za su kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ezekiel 32 >