< 2 Samuel 3 >

1 Now there was a long war between Saul's people and David's people; and David became stronger and stronger, but those on Saul's side became more and more feeble.
Aka daɗe ana yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda. Dawuda kuwa ya yi ta ƙara ƙarfi, yayinda gidan Shawulu ya yi ta raguwa a ƙarfi.
2 While David was in Hebron he became the father of sons: the oldest was Amnon, son of Ahinoam of Jezreel;
An haifa wa Dawuda’ya’ya maza a Hebron. Ɗansa na fari shi ne Amnon, ɗan Ahinowam mutuniyar Yezireyel;
3 And the second, Chileab, whose mother was Abigail, the wife of Nabal the Carmelite; and the third, Absalom, son of Maacah, the daughter of Talmai, king of Geshur;
na biyu shi ne Kileyab, ɗan Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel; na uku shi ne Absalom, ɗan Ma’aka’yar Talmai sarkin Geshur;
4 And the fourth, Adonijah, the son of Haggith; and the fifth, Shephatiah, the son of Abital;
na huɗu shi ne Adoniya, ɗan Haggit; na biyar shi ne Shefatiya, ɗan Abital;
5 And the sixth, Ithream, whose mother was David's wife Eglah. These were the sons of David, whose birth took place in Hebron.
na shida kuma shi ne Itireyam, ɗan Egla matar Dawuda. An haifi waɗannan wa Dawuda a Hebron.
6 Now while there was war between Saul's people and David's people, Abner was making himself strong among the supporters of Saul.
Sa’ad da ake yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda, sai Abner ya yi ta ƙarfafa matsayinsa a gidan Shawulu.
7 Now Saul had among his wives a woman named Rizpah, the daughter of Aiah: and Ish-bosheth said to Abner, Why have you taken my father's wife?
To, Shawulu yana da ƙwarƙwarar da ake kira Rizfa,’yar Aiya. Sai Ish-Boshet ya ce wa Abner, “Don me kake kwana da ƙwarƙwarar mahaifina?”
8 And Abner was very angry at the words of Ish-bosheth, and he said, Am I a dog's head of Judah? I am this day doing all in my power for the cause of your father Saul and for his brothers and his friends, and have not given you up into the hands of David, and now you say I have done wrong with a woman.
Abner ya husata saboda abin da Ish-Boshet ya ce, sai ya ce, “Kana tsammani ni mai cin amana ne? Kana zato ni mai goyon bayan Yahuda ne? Tun farko na nuna aminci ga gidan babanka Shawulu, da’yan’uwansa, da abokansa! Ban kuwa ba da kai a hannun Dawuda ba. Ga shi yanzu a kan mace za ka ga laifina?
9 May God's punishment be on Abner, if I do not for David as the Lord in his oath has said,
Allah yă yi wa Abner hukunci mai tsanani, in ban goyi bayan Dawuda ya sami abin da Ubangiji ya yi masa alkawari da rantsuwa ba.
10 And if I do not take away the kingdom from the family of Saul and make David ruler over Israel and Judah from Dan as far as Beer-sheba!
Zan kuma mayar wa Dawuda sarautar gidan Shawulu, in kafa kursiyin Dawuda a kan Isra’ila, da kan Yahuda tun daga Dan har zuwa Beyersheba.”
11 And so great was Ish-bosheth's fear of Abner that he was not able to say a word in answer.
Ish-Boshet bai ƙara yin karambanin ce wa Abner kome ba, gama yana tsoronsa.
12 And Abner sent men to David at Hebron, saying, Make an agreement with me, and I will give you my support in getting all Israel on your side.
Sai Abner ya aiki manzanni a madadinsa wurin Dawuda su ce masa, “Ƙasar ta wane ne? Ka yi yarjejjeniya da ni, zan kuwa taimake ka, in juye dukan Isra’ila zuwa ɓangarenka.”
13 And he said, It is well; I will make an agreement with you, but on one condition, which is, that when you come before me, Saul's daughter Michal is to come with you; till she comes you will not see my face.
Dawuda ya ce, “Da kyau, zan yi yarjejjeniya da kai, amma fa ina bukata abu guda daga gare ka, kada ka zo gabana in ba tare da matata Mikal,’yar Shawulu ba.”
14 And David sent men to Saul's son Ish-bosheth, saying, Give me back Michal, my wife, whom I made mine for the price of the private parts of a hundred Philistines.
Sai Dawuda ya aiki manzanni zuwa wurin Ish-Boshet ɗan Shawulu cewa, “Ka ba ni matata Mikal wadda na biya sadakinta da loɓa ɗari na Filistiyawa.”
15 So Ish-bosheth sent and took her from her husband Paltiel, the son of Laish.
Sai Ish-Boshet ya ba da umarni, aka kuwa ɗauke ta daga gidan mijinta Faltiyel ɗan Layish.
16 And her husband went with her as far as Bahurim, weeping while he went. Then Abner said to him, Go back. And he went back.
Amma mijin ya raka ta, yana tafe yana kuka, ya bi ta har Bahurim. Sai Abner ya ce masa, “Koma gida!” Sai ya koma.
17 Then Abner had a talk with the chief men of Israel, saying, In the past it was your desire to make David your king: so now, do it:
Abner ya tattauna da dattawan Isra’ila ya ce, “An daɗe kuna nema ku naɗa Dawuda sarkinku.
18 For the Lord has said of David, By the hand of my servant David I will make my people Israel safe from the Philistines, and from all who are against them.
To, yanzu sai ku yi haka! Gama Ubangiji ya yi wa Dawuda alkawari ya ce, ‘Ta wurin bawana Dawuda zan ceci mutanena Isra’ila daga hannun Filistiyawa, da kuma hannun dukan abokan gābansu.’”
19 And Abner said the same things to Benjamin: and he went to David in Hebron to make clear to him what seemed good to Israel and to all the people of Benjamin.
Abner kuma ya yi magana da mutane Benyamin da kansa. Sa’an nan ya tafi Hebron yă gaya wa Dawuda ko mene ne Isra’ila da kuma dukan gidan Benyamin suke so su yi.
20 So Abner, with twenty men, came to Hebron, to David. And David made a feast for Abner and the men who were with him.
Sa’ad da Abner wanda yake tare da mutane ashirin suka zo wurin Dawuda a Hebron, Dawuda ya shirya masa liyafa tare da mutanensa.
21 And Abner said to David, Now I will go, and make all Israel come to my lord the king, so that they may make an agreement with you, and your kingdom may be as wide as your heart's desire. Then David sent Abner away and he went in peace.
Sai Abner ya ce wa Dawuda, “Bari in tafi nan da nan in tattara dukan Isra’ila wa ranka yă daɗe, sarki, saboda su yi alkawari da kai, ka kuma ka yi mulki bisa dukansu yadda ranka yake so.” Saboda haka Dawuda ya sallami Abner, ya kuwa tafi lafiya.
22 Now the servants of David and Joab had been out attacking a band of armed men, and they came back with a great store of goods taken in the fight: but Abner was no longer in Hebron with David, for he had sent him away and he had gone in peace.
Ba a jima ba sai mutanen Dawuda da Yowab suka dawo daga hari. Suka kawo ganima da yawa tare da su. Abner kuwa ya riga ya bar Dawuda a Hebron, domin Dawuda ya sallame shi, shi kuma ya tafi lafiya.
23 When Joab and his men came, news was given them that Abner, the son of Ner, had come to the king, who had let him go away again in peace.
Sa’ad da Yowab da dukan sojoji suka dawo, aka gaya masa cewa Abner ɗan Ner ya zo wurin sarki, sarki kuwa ya sallame shi, ya kuma tafi lafiya.
24 Then Joab came to the king, and said, What have you done? when Abner came to you why did you send him away and let him go?
Sai Yowab ya je wurin sarki ya ce, “Me ke nan ka yi? Abner ya zo wurinka. Don me ka ƙyale shi yă tafi? Ga shi kuwa ya tafi!
25 Is it not clear to you that Abner, the son of Ner, came with deceit to get knowledge of your going out and your coming in and of all you are doing?
Ka san Abner ɗan Ner ya zo ne yă ruɗe ka, yă ga fitarka da shigarka, yă kuma binciki kome da kake yi.”
26 And when Joab had come out from David, he sent men after Abner, and they overtook him at the water-spring of Sirah, and made him come back with them: but David had no knowledge of it.
Yowab ya tashi daga gaban Dawuda ya tafi ya aika manzanni su bi Abner. Suka same shi a rijiyar Sira suka komo da shi, Dawuda kuwa bai sani ba.
27 And when Abner was back in Hebron, Joab took him on one side by the doorway of the town to have a word with him quietly, and there he gave him a wound in the stomach, causing his death in payment for the death of his brother Asahel.
To, da Abner ya komo Hebron, Yowab ya ratse da shi zuwa hanyar shigar gari kamar zai gana da shi a kaɗaice. Amma a can ya soki Abner a ciki, ya kashe shi don yă rama mutuwar ɗan’uwansa Asahel.
28 And when David had word of it he said, May I and my kingdom be clear for ever in the eyes of the Lord from the blood of Abner, the son of Ner:
Daga baya, Dawuda ya ji labarin sai ya ce, “Ni da masarautata har abada ba mu da laifi a gaban Ubangiji game da jinin Abner ɗan Ner.
29 May it come on the head of Joab and all his father's family: among the men of Joab's family may there ever be some who are diseased or lepers, or who do the work of women, or are put to the sword, or are wasted from need of food!
Alhakin jininsa yă kasance a kan Yowab da kuma a kan dukan iyalin mahaifinsa! Kada gidan Yowab yă rasa mai ɗiga, ko kuturu, ko mai jingina ga sanda, ko wanda aka kashe da takobi, ko kuma wanda ba shi da abinci.”
30 So Joab and Abishai his brother put Abner to death, because he had put to death their brother Asahel in the fight at Gibeon.
(Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka kashe Abner don yă kashe ɗan’uwansu Asahel a yaƙin Gibeyon.)
31 And David said to Joab and all the people who were with him, Go in grief and put haircloth about you, in sorrow for Abner. And King David went after the dead body.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa Yowab da dukan mutanen da suke tare da shi, “Ku yayyage rigunarku, ku sa tsummoki, ku yi tafiya kuna kuka a gaban Abner.” Sarki Dawuda kansa ya bi masu ɗauke da gawar daga baya.
32 And they put Abner's body to rest in Hebron; and the king and all the people were weeping loudly by the resting-place of Abner's body.
Suka binne Abner a Hebron, sarki kuwa ya ɗaga murya ya yi kuka a kabarin Abner.
33 And the king made a song of grief for Abner and said, Was the death of Abner to be like the death of a foolish man?
Sarki ya kuma yi wannan waƙar makoki domin Abner ya ce, “Daidai ne Abner yă mutu, kamar yadda marasa bin doka suke mutuwa?
34 Your hands were free, your feet were not chained: like the downfall of a man before evil men, so was your fall. And the weeping of the people over him went on again.
Hannuwanka ba a daure suke ba, ƙafafunka ba a tabaibaye suke ba. Ka mutu kamar waɗanda suke mutuwa a hannun mugaye.” Sai dukan mutane suka sāke fashe da kuka saboda shi.
35 And the people came to make David take food, while it was still day, but David with an oath said, May God's punishment be on me if I take a taste of bread or any other thing till the sun has gone down!
Sa’an nan duk suka zo suka roƙi Dawuda yă ci wani abu tun rana ba tă fāɗi ba; amma Dawuda ya rantse ya ce, “Bari Allah yă hukunta ni, in na ɗanɗana abinci ko wani abu kafin rana ta fāɗi!”
36 And all the people took note of it and were pleased: like everything the king did, it was pleasing to the people.
Dukan mutane suka lura suka kuma ji daɗi ƙwarai, tabbatacce kome da sarki ya yi, ya gamshe su.
37 So it was clear to Israel and to all the people on that day that the king was not responsible for the death of Abner, the son of Ner.
Saboda haka a ranar dukan mutane da dukan Isra’ila suka gane sarki ba shi da hannu a kisan Abner ɗan Ner.
38 And the king said to his servants, Do you not see that a chief and a great man has come to his end today in Israel?
Sa’an nan sarki ya ce wa mutanensa, “Ba ku gane cewa ɗan sarki kuma babban mutum ya mutu a ƙasar Isra’ila a yau ba?
39 While I, though I am crowned king, have little strength, and these men, the sons of Zeruiah, are out of my control: may the Lord give to the evil-doer the reward of his evil-doing!
A yau, ko da yake ni naɗaɗɗen sarki ne, duk da haka na raunana, kuma waɗannan’ya’yan Zeruhiya sun fi ƙarfina. Ubangiji yă sāka wa mai aikata mugunta da muguntar da ya aikata!”

< 2 Samuel 3 >