< 2 Samuel 1 >

1 Now after the death of Saul, when David, having come back from the destruction of the Amalekites, had been in Ziklag for two days;
Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
2 On the third day a man came from Saul's tents, with his clothing out of order and earth on his head: and when he came to David, he went down on the earth and gave him honour.
A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
3 And David said to him, Where have you come from? And he said, I have come in flight from the tents of Israel.
Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
4 And David said to him, How did things go? Give me the news. And in answer he said, The people have gone in flight from the fight, and a great number of them are dead; and Saul and his son Jonathan are dead.
Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
5 And David said to the young man who gave him the news, Why are you certain that Saul and his son Jonathan are dead?
Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
6 And the young man said, I came by chance to Mount Gilboa, and I saw Saul supporting himself on his spear; and the war-carriages and horsemen overtook him.
Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
7 And looking back, he saw me and gave a cry to me. And answering him I said, Here am I.
Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
8 And he said to me, Who are you? And I said, I am an Amalekite.
“Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
9 Then he said to me, Come here to my side, and put me to death, for the pain of death has me in its grip but my life is still strong in me.
“Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
10 So I put my foot on him and gave him his death-blow, because I was certain that he would not go on living after his fall: and I took the crown from his head and the band from his arm, and I have them here for my lord.
“Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
11 Then David gave way to bitter grief, and so did all the men who were with him:
Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
12 And till evening they gave themselves to sorrow and weeping, and took no food, weeping for Saul and for Jonathan, his son, and for the people of the Lord and for the men of Israel; because they had come to their end by the sword.
Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
13 And David said to the young man who had given him the news, Where do you come from? And he said, I am the son of a man from a strange land; I am an Amalekite.
Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
14 And David said to him, Had you no fear of stretching out your hand to put to death the one marked with the holy oil?
Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
15 And David sent for one of his young men and said, Go near and put an end to him. And he put him to death.
Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
16 And David said to him, May your blood be on your head; for your mouth has given witness against you, saying, I have put to death the man marked with the holy oil.
Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
17 Then David made this song of grief for Saul and Jonathan, his son:
Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
18 (It is recorded in the book of Jashar for teaching to the sons of Judah) and he said:
Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
19 The glory, O Israel, is dead on your high places! How have the great ones been made low!
“Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
20 Give no news of it in Gath, let it not be said in the streets of Ashkelon; or the daughters of the Philistines will be glad, the daughters of men without circumcision will be uplifted in joy.
“Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
21 O mountains of Gilboa, let there be no dew or rain on you, you fields of death: for there the arms of the strong have been shamed, the arms of Saul, as if he had not been marked with the holy oil.
“Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
22 From the blood of the dead, from the fat of the strong, the bow of Jonathan was not turned back, the sword of Saul did not come back unused.
“Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
23 Saul and Jonathan were loved and pleasing; in their lives and in their death they were not parted; they went more quickly than eagles, they were stronger than lions.
Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
24 O daughters of Israel, have sorrow for Saul, by whom you were delicately clothed in robes of red, with ornaments of gold on your dresses.
“Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
25 How have the great ones been made low in the fight! Jonathan is dead on your high places.
“Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
26 I am full of grief for you, my brother Jonathan: very dear have you been to me: your love for me was a wonder, greater than the love of women.
Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
27 How have the great ones been made low, and the arms of war broken!
“Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”

< 2 Samuel 1 >