< 2 Kings 13 >

1 In the twenty-third year of Joash, the son of Ahaziah, king of Judah, Jehoahaz, the son of Jehu, became king over Israel in Samaria, ruling for seventeen years.
A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
2 He did evil in the eyes of the Lord, copying the sins of Jeroboam, the son of Nebat, which he did and made Israel do; he did not keep himself from them.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
3 So the wrath of the Lord was burning against Israel, and he gave them up into the power of Hazael, king of Aram, and into the power of Ben-hadad, the son of Hazael, again and again.
Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
4 Then Jehoahaz made prayer to the Lord, and the Lord gave ear to him, for he saw how cruelly Israel was crushed by the king of Aram.
Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
5 (And the Lord gave Israel a saviour, so that they became free from the hands of the Aramaeans; and the children of Israel were living in their tents as in the past.
Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
6 But still they did not give up the sin of Jeroboam, which he made Israel do, but went on with it; and there was an image of Asherah in Samaria.)
Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
7 For out of all his army, Jehoahaz had only fifty horsemen and ten carriages and ten thousand footmen; the king of Aram had given them up to destruction, crushing them like dust.
Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
8 Now the rest of the acts of Jehoahaz, and all he did, and his great power, are they not recorded in the book of the history of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
9 And Jehoahaz went to rest with his fathers, and was put into the earth in Samaria; and Joash his son became king in his place.
Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
10 In the thirty-seventh year of the rule of Joash, king of Judah, Joash, the son of Jehoahaz, became king over Israel in Samaria, ruling for sixteen years.
A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
11 He did evil in the eyes of the Lord, not turning away from the sin of Jeroboam, the son of Nebat, which he did and made Israel do, but he went on with it.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
12 Now the rest of the acts of Joash, and all he did, and the force with which he went to war against Amaziah, king of Judah, are they not recorded in the book of the history of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
13 And Joash went to rest with his fathers and Jeroboam took his place as king; and Joash was put into the earth in Samaria with the kings of Israel.
Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
14 Now Elisha became ill with the disease which was the cause of his death: and Joash, king of Israel, came down to him, and weeping over him said, My father, my father, the war-carriages of Israel and its horsemen!
To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
15 Then Elisha said to him, Take bow and arrows: and he took bow and arrows.
Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
16 And he said to the king of Israel, Put your hand on the bow: and he put his hand on it; and Elisha put his hands on the king's hands.
Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
17 Then he said; Let the window be open to the east: and he got it open. Then Elisha said, Let the arrow go; and he let it go. And he said, The Lord's arrow of salvation, of salvation over Aram; for you will overcome the Aramaeans in Aphek and put an end to them.
Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
18 And he said, Take the arrows: and he took them. And he said to the king of Israel, Send them down into the earth; and he did so three times and no more.
Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
19 Then the man of God was angry with him and said, If you had done it five or six times, then you would have overcome Aram completely; but now you will only overcome them three times.
Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
20 And death came to Elisha and they put his body into the earth. Now in the spring of the year, armed bands of Moabites frequently came, overrunning the land.
Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
21 And while they were putting a dead man into the earth, they saw a band coming; and they put the man quickly into the place where Elisha's body was; and the dead man, on touching Elisha's bones, came to life again, and got up on his feet.
Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
22 And Israel was crushed under the power of Hazael, king of Aram, all the days of Jehoahaz.
Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
23 But the Lord was kind to them and had pity on them, caring for them, because of his agreement with Abraham, Isaac, and Jacob; he would not put them to destruction or send them away from before his face till now.
Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
24 Then Hazael, king of Aram, came to his end; and Ben-hadad his son became king in his place.
Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
25 And Jehoash, the son of Jehoahaz, took again from Ben-hadad, the son of Hazael, the towns which he had taken from Jehoahaz his father in war. Three times Jehoash overcame him and got back the towns of Israel.
Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.

< 2 Kings 13 >