< Luke 1 >

1 Since many have undertaken to compose a history of the things that are fully believed among us,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 even as they were delivered to us by those who were, from the beginning, eye-witnesses and ministers of the word;
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 it seemed good to me also, having obtained exact information of all things from the very first, to write them in order for you, most excellent Theophilus,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 that you might know the certainty of the things in which you have been instructed.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 There was, in the days of Herod the king of Judea, a certain priest, named Zachariah, of the class of Abijah; and his wife was of the daughters of Aaron, and her name was Elizabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 They were both righteous before God, walking in all the commandments and ordinances of the Lord, blameless.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 And they had no child, because Elizabeth was barren, and they were both advanced in years.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 It came to pass, while he was officiating as priest before God, in the order of his class, that,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 according to the custom of the priest’s office, his lot was to burn incense, when he went into the temple of the Lord.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 And all the multitude of the people were praying without, at the time of incense.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 And there appeared to him an angel of the Lord, standing at the right side of the altar of incense.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 And Zachariah was troubled at the sight, and fear fell upon him.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 But the angel said to him: Fear not, Zachariah; for your prayer is heard, and your wife Elizabeth shall bear you a son, and you shall call his name John.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 And you shall have joy and gladness, and many shall rejoice at his birth.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 For he shall be great before the Lord; and he shall drink neither wine nor strong drink; and he shall be filled with the Holy Spirit even from his mother’s womb.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 And many of the sons of Israel shall he turn to the Lord their God.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 And he shall go before him in the spirit and power of Elijah to turn the hearts of the fathers to the children, and the disobedient, by the wisdom of the just, in order to make ready for the Lord a prepared people.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 And Zachariah said to the angel: By what sign shall I know this? for I am old, and my wife is advanced in years.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 And the angel answered and said to him: I am Gabriel, who stands in the presence of God; and I am sent to speak to you, and to announce to you this good news.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 And behold, you shall be dumb and not able to speak, till the day in which these things shall take place, because you did not believe my words, which shall be fulfilled in their proper time.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 And the people were waiting for Zachariah, and they wondered that he stayed so long in the temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 But when he came out, he was not able to speak to them; and they perceived that he had seen a vision in the temple; and he made signs to them, and remained speechless.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 And it came to pass, when the days of his service were completed, that he departed to his own house.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 And after those days, his wife Elizabeth conceived, and kept herself retired for five months, saying:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Thus has the Lord dealt with me in the days in which he has looked with regard upon me, to take away my reproach among men.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 And in the sixth month, the angel Gabriel was sent from God into a city of Galilee, named Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 to a virgin betrothed to a man whose name was Joseph, of the house of David; and the name of the virgin was Mary.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 And the angel came into her presence, and said: Hail, graciously accepted: the Lord is with you; blessed are you among women.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 And she was perplexed at his words, and reasoned, what this salutation could mean.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 And the angel said to her: Fear not, Mary; for you have found favor with God.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 And behold, you shall conceive and bear a son, and you shall call his name Jesus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 He shall be great, and shall be called the Son of the Most High; and the Lord God will give to him the throne of David his father;
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 and he shall reign over the house of Jacob forever, and of his kingdom there shall be no end. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 But Mary said to the angel: How shall this be, since I know not a man?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 And the angel answered and said to her: The Holy Spirit will come upon you, and the power of the Most High will overshadow you; for which reason, also, that which is begotten, being holy, shall be called the Son of God.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 And behold, Elizabeth your kinswoman, even she has conceived a son in her old age; and this is the sixth month with her who is called barren;
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 for nothing shall be impossible with God.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 And Mary said: Behold the handmaid of the Lord; let it be to me according to your word. And the angel departed from her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 And Mary arose in those days, and went with haste into the mountainous country, into a city of Judah;
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 and she came into the house of Zachariah, and saluted Elizabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 And it came to pass, when Elizabeth heard the salutation of Mary, that the babe in her womb leaped for joy.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 And Elizabeth was filled with the Holy Spirit, and spoke with a loud voice, and said: Blessed are you among women, and blessed is the fruit of your womb.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 And whence is this to me, that the mother of my Lord should come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For, behold, when the voice of your salutation sounded in my ears, the babe in my womb leaped for joy.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 And blessed is she who believed; for there shall be a fulfillment of the things which were spoken to her from the Lord.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 And Mary said: My soul magnifies the Lord,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 and my spirit rejoices in God, my Savior;
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 for he has looked upon the lowly condition of his handmaid. For, behold, from this time, all generations shall call me blessed;
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 for He that is Mighty has done great things for me, and holy is his name:
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 and his mercy is from generation to generation upon those who fear him.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He has done mighty deeds with his arm; he has scattered those who are proud in the understanding of their hearts.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He has cast down the mighty from their thrones, and exalted the lowly.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 He has filled the hungry with good things, but the rich he has sent empty away.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 He has helped Israel his servant, (as he spoke to our fathers, )
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 by remembering his mercy to Abraham and to his posterity forever. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 And Mary remained with her about three months, and returned to her own house.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Now the time for Elizabeth to be delivered had fully come; and she gave birth to a son.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 And her neighbors and relatives heard that the Lord had showed great mercy to her, and they rejoiced with her.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 And it came to pass, on the eighth day, that they came to circumcise the child; and they called him by the name of his father, Zachariah.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 And his mother answered and said: Not so: but he shall be called John.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 And they said to her: There is no one among your relatives that is called by this name.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 And they made signs to his father, to know what he wished him to be called.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 And having asked for a writing tablet, he wrote, saying: His name is John. And they were all astonished.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 And immediately his mouth was opened, and his tongue was loosed, and he spoke, and praised God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 And fear came on all that dwelt round about them; and all these things were talked of everywhere throughout the mountainous country of Judea.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 And all that heard them, laid them up in their hearts, and said: What, then, will this child be? And the hand of the Lord was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 And Zachariah his father was filled with the Holy Spirit, and prophesied, saying:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Blessed be the Lord God of Israel; for he has visited and redeemed his people;
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 and he has raised up for us, in the house of David his servant, a horn of salvation,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 (as he spoke by the mouth of all his holy prophets of ancient times, ) (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 salvation from our enemies, and from the hand of all that hate us,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 in order to show the mercy promised to our fathers, and to remember his holy covenant,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 the oath which he swore to Abraham our father,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 that he would grant to us, that being delivered from the hands of our enemies, we might serve him without fear,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 in holiness and righteousness before him, all our days.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And you, child, shall be called the prophet of the Most High; for you shall go before the face of the Lord, to make ready his ways,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 by giving to his people the knowledge of salvation in the remission of their sins,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 through the tender mercies of our God; by which the dawn from on high has visited us,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 to give light to those who sit in darkness and in the shadow of death, by guiding our feet in the way of peace.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And the child grew and became strong in spirit; and he was in the deserts till the day of his manifestation to Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >