< Joshua 14 >

1 And these are the inheritances which the children of Israel took in the land of Canaan, which Eleazar the priest, and Joshua the son of Nun, and the heads of the fathers’ [houses] of the tribes of the children of Israel, distributed unto them,
Ga wuraren da Isra’ilawa suka sami gādo a ƙasar Kan’ana waɗanda Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin iyalai kabila-kabila na Isra’ila suka raba musu.
2 by the lot of their inheritance, as Jehovah commanded by Moses, for the nine tribes, and for the half-tribe.
Ta wurin yin ƙuri’a aka raba wa kabilan nan tara da rabi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
3 For Moses had given the inheritance of the two tribes and the half-tribe beyond the Jordan: but unto the Levites he gave no inheritance among them.
Musa ya ba wa kabilan biyu da rabin nan gādonsu gabashin Urdun, amma bai ba wa Lawiyawa gādo a cikin sauran ba,
4 For the children of Joseph were two tribes, Manasseh and Ephraim: and they gave no portion unto the Levites in the land, save cities to dwell in, with the suburbs thereof for their cattle and for their substance.
gama’ya’yan Yusuf sun zama kabilu biyu, Manasse da Efraim. Ba a ba Lawiyawa gādon ba sai dai garuruwan da aka ba su su zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau domin dabbobinsu.
5 As Jehovah commanded Moses, so the children of Israel did; and they divided the land.
Haka Isra’ilawa suka raba ƙasar, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
6 Then the children of Judah drew nigh unto Joshua in Gilgal: and Caleb the son of Jephunneh the Kenizzite said unto him, Thou knowest the thing that Jehovah spake unto Moses the man of God concerning me and concerning thee in Kadesh-barnea.
Mutanen Yahuda kuma suka je wurin Yoshuwa a Gilgal, sai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze ya ce wa Yoshuwa, “Ka san abin da Ubangiji ya gaya wa Musa, mutumin Allah a Kadesh Barneya game da kai da ni.
7 Forty years old was I when Moses the servant of Jehovah sent me from Kadesh-barnea to spy out the land; and I brought him word again as it was in my heart.
Ina da shekara arba’in lokacin da Musa bawan Ubangiji ya aike ni zuwa Kadesh Barneya in leƙi asirin ƙasar. Na kuwa kawo masa rahoto daidai yadda na ga ƙasar,
8 Nevertheless my brethren that went up with me made the heart of the people melt; but I wholly followed Jehovah my God.
amma’yan’uwana waɗanda muka je tare su suka ba da rahoton da ya sa zukatan mutane suka narke don tsoro. Ni kam na bi Ubangiji Allah da dukan zuciyata.
9 And Moses sware on that day, saying, Surely the land whereon thy foot hath trodden shall be an inheritance to thee and to thy children for ever, because thou hast wholly followed Jehovah my God.
Saboda haka a ranan nan Musa ya rantse mini cewa, ‘Ƙasar da ka taka za tă zama ƙasarka ta gādo kai da’ya’yanka har abada, domin ka bi Ubangiji Allahna da dukan zuciyarka.’
10 And now, behold, Jehovah hath kept me alive, as he spake, these forty and five years, from the time that Jehovah spake this word unto Moses, while Israel walked in the wilderness: and now, lo, I am this day fourscore and five years old.
“Ga shi, kamar yadda Ubangiji ya yi alkawari, ya bar ni da rai har na ƙara shekaru arba’in da biyar tun daga lokacin da ya gaya wa Musa wannan, a lokacin da Isra’ilawa suke yawo a cikin jeji. Ga ni nan yau shekaruna tamanin da biyar!
11 As yet I am as strong this day as I was in the day that Moses sent me: as my strength was then, even so is my strength now, for war, and to go out and to come in.
Ina nan da ƙarfina kamar yadda nake da ƙarfi a lokacin da Musa ya aike ni; zan iya fita zuwa yaƙi da ƙwazo yanzu kamar yadda nake zuwa a dā.
12 Now therefore give me this hill-country, whereof Jehovah spake in that day; for thou heardest in that day how the Anakim were there, and cities great and fortified: it may be that Jehovah will be with me, and I shall drive them out, as Jehovah spake.
Yanzu sai ka ba ni wannan ƙasar da take kan tudu wadda Ubangiji ya yi alkawari zai ba ni a ranan nan. Kai ma ka ji a lokacin, yadda Anakawa suke a can, biranensu manya ne kuma sun kewaye su sosai, amma na sani Ubangiji zai taimake ni, zan kore su kamar yadda ya faɗa.”
13 And Joshua blessed him; and he gave Hebron unto Caleb the son of Jephunneh for an inheritance.
Sai Yoshuwa ya sa wa Kaleb ɗan Yefunne albarka, ya ba shi Hebron.
14 Therefore Hebron became the inheritance of Caleb the son of Jephunneh the Kenizzite unto this day; because that he wholly followed Jehovah, the God of Israel.
Saboda haka Hebron ta zama ƙasar Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze tun daga lokacin nan, domin ya bi Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa.
15 Now the name of Hebron beforetime was Kiriath-arba; [which Arba was] the greatest man among the Anakim. And the land had rest from war.
(Dā a kan kira wannan Hebron, Kiriyat Arba. Wannan Arba kuwa shi ne wani katon mutum a cikin Anakawa.) Sa’an nan ƙasar ta huta daga yaƙi.

< Joshua 14 >