< Amos 6 >

1 Woe to them that are at ease in Zion, and to them that are secure in the mountain of Samaria, the notable men of the chief of the nations, to whom the house of Israel come!
Taku ta ƙare, ku da kuke zaman sakewa a Sihiyona, da ku waɗanda kuke ji zama a Dutsen Samariya lafiya ne, ku manyan mutanen ƙasar da take sananniya, waɗanda mutanen Isra’ila suke zuwa!
2 Pass ye unto Calneh, and see; and from thence go ye to Hamath the great; then go down to Gath of the Philistines: are they better than these kingdoms? or is their border greater than your border?
Ku je Kalne ku dube ta; ku wuce daga can zuwa Hamat-rabba, sa’an nan ku gangara zuwa Gat a Filistiya. Sun fi masarautunku biyu ne? Ƙasarsu ta fi taku girma?
3 —ye that put far away the evil day, and cause the seat of violence to come near;
Kuna ƙoƙari ku kauce wa wannan muguwar rana kuna kuma jawo mulkin tashin hankali kusa.
4 that lie upon beds of ivory, and stretch themselves upon their couches, and eat the lambs out of the flock, and the calves out of the midst of the stall;
Kuna kwanciya a kan gadajen da aka yi musu shimfiɗar hauren giwa kuna mimmiƙe a kan kujerunku. Kuna cin naman ƙibabbun raguna da na ƙosassun’yan maruƙa.
5 that sing idle songs to the sound of the viol; that invent for themselves instruments of music, like David;
Kuna kaɗa molayenku yadda Dawuda ya yi kuna ƙirƙiro waƙoƙi a kan kayan kaɗe-kaɗe.
6 that drink wine in bowls, and anoint themselves with the chief oils; but they are not grieved for the affliction of Joseph.
Da manyan kwanoni kuke shan ruwan inabi kuna kuma shafa mai mafi kyau, amma ba kwa baƙin ciki game da kangon da Yusuf ya zama.
7 Therefore shall they now go captive with the first that go captive; and the revelry of them that stretched themselves shall pass away.
Saboda haka za ku zama na farkon da za su tafi zaman bauta; bukukkuwanku da shagulgulanku za su ƙare.
8 The Lord Jehovah hath sworn by himself, saith Jehovah, the God of hosts: I abhor the excellency of Jacob, and hate his palaces; therefore will I deliver up the city with all that is therein.
Ubangiji Mai Iko Duka da kansa ya rantse, Ubangiji Allah Maɗaukaki ya furta, “Ina ƙyamar girman kan Yaƙub, ba na kuma son kagarunsa; zan ba da birnin da duk abin da yake cikinta.”
9 And it shall come to pass, if there remain ten men in one house, that they shall die.
Ko da mutum goma ne suka ragu a gida guda, su ma za su mutu.
10 And when a man’s uncle shall take him up, even he that burneth him, to bring out the bones out of the house, and shall say unto him that is in the innermost parts of the house, Is there yet any with thee? and he shall say, No; then shall he say, Hold thy peace; for we may not make mention of the name of Jehovah.
In kuma wani dangi ya shiga don yă fitar da gawawwakin yă ƙone ya kuwa tambayi wani wanda yake ɓoye a can, yana cewa, “Akwai wani tare da kai?” Ya kuwa ce, “Babu,” sai yă ce, “Kul! Kada mu ambaci sunan Ubangiji.”
11 For, behold, Jehovah commandeth, and the great house shall be smitten with breaches, and the little house with clefts.
Gama Ubangiji ya ba da umarni, zai kuma ragargaza babban gidan nan kucu-kucu ƙaramin gidan kuwa zai yi rugu-rugu da shi.
12 Shall horses run upon the rock? will one plow [there] with oxen? that ye have turned justice into gall, and the fruit of righteousness into wormwood;
Dawakai sukan yi gudu a kan duwatsu? Wani yana iya yin noma a teku da shanun noma? Amma ga shi kun mai da gaskiya ta zama dafi amfanin adalci kuma ya zama ɗaci,
13 ye that rejoice in a thing of nought, that say, Have we not taken to us horns by our own strength?
ku da kuke murna saboda an ci Lo Debar da yaƙi kuka kuma ce, “Ba da ƙarfinmu ne muka ƙwace Karnayim ba?”
14 For, behold, I will raise up against you a nation, O house of Israel, saith Jehovah, the God of hosts; and they shall afflict you from the entrance of Hamath unto the brook of the Arabah.
Gama Ubangiji Allah Maɗaukaki ya ce, “Zan sa wata ƙasa ta tayar muku, ya ku gidan Isra’ila, wadda za tă matsa muku tun daga Lebo Hamat zuwa kwarin Araba.”

< Amos 6 >