< Romans 8 >

1 There is therefore now no condemnation to those who are in Christ Jesus, who do not walk according to the flesh, but according to the Spirit.
Saboda haka, yanzu babu hukunci don waɗanda suke cikin Kiristi Yesu,
2 For the law of the Spirit of life in Christ Jesus made me free from the law of sin and of death.
gama ta wurin Kiristi Yesu dokar Ruhu mai ba da rai ta’yantar da ni daga Dokar Musa.
3 For what the law could not do, in that it was weak through the flesh, God did, sending his own Son in the likeness of sinful flesh and for sin, he condemned sin in the flesh,
Gama abin da dokar ba tă iya yi saboda kāsawar mutuntaka ba, Allah ya yi shi sa’ad da ya aiko da Ɗansa a kamannin mutum mai zunubi, don yă zama hadaya ta zunubi. Ta haka, ya hukunta zunubi a cikin mutum mai zunubi.
4 that the ordinance of the law might be fulfilled in us who do not walk according to the flesh, but according to the Spirit.
Ya yi haka domin yă cika bukatun adalcin doka a cikinmu, mu da ba ma rayuwa bisa ga mutuntaka, sai dai bisa ga Ruhu.
5 For those who live according to the flesh set their minds on the things of the flesh, but those who live according to the Spirit, the things of the Spirit.
Waɗanda suke rayuwa bisa ga mutuntaka sun kafa hankulansu a kan sha’awace-shawa’acen jiki; amma waɗanda suke rayuwa bisa ga Ruhu sun kafa hankulansu a kan abubuwan da Ruhu yake so.
6 For the mind of the flesh is death, but the mind of the Spirit is life and peace;
Ƙwallafa rai ga al’amuran halin mutuntaka ƙarshensa mutuwa ne, ƙwallafa rai ga al’amuran Ruhu kuwa rai ne da salama;
7 because the mind of the flesh is hostile toward God, for it is not subject to God’s law, neither indeed can it be.
hankalin mai zunubi na gāba da Allah. Ba ya biyayya da dokar Allah, ba kuwa zai iya yin haka ba.
8 Those who are in the flesh cannot please God.
Waɗanda mutuntaka yake mulkinsu ba za su iya su gamshi Allah ba.
9 But you are not in the flesh but in the Spirit, if it is so that the Spirit of God dwells in you. But if any man does not have the Spirit of Christ, he is not his.
Ku kam, ana mulkinku ba ta wurin mutuntaka ba, sai dai ta wurin Ruhu, in Ruhun Allah yana zaune a cikinku. In kuma wani ba shi da Ruhun Kiristi, shi ba na Kiristi ba ne.
10 If Christ is in you, the body is dead because of sin, but the spirit is alive because of righteousness.
Amma in Kiristi yana a cikinku, jikinku matacce ne saboda zunubi, duk da haka ruhunku yana a raye saboda adalci.
11 But if the Spirit of him who raised up Jesus from the dead dwells in you, he who raised up Christ Jesus from the dead will also give life to your mortal bodies through his Spirit who dwells in you.
In kuwa Ruhu wannan da ya tā da Yesu daga matattu yana zama a cikinku, shi wanda ya tā da Kiristi daga matattu zai ba da rai ga jikunanku masu mutuwa ta wurin Ruhunsa, wanda yake zama a cikinku.
12 So then, brothers, we are debtors, not to the flesh, to live after the flesh.
Saboda haka’yan’uwa, muna da hakki, amma ba na wanda za mu yi rayuwar mutuntaka da yake so ba.
13 For if you live after the flesh, you must die; but if by the Spirit you put to death the deeds of the body, you will live.
Gama in kuna rayuwa bisa ga mutuntaka, za ku mutu; amma in ta wurin Ruhu kuka kashe ayyukan jikin nan, za ku rayu.
14 For as many as are led by the Spirit of God, these are children of God.
Domin waɗanda Ruhun Allah yake bi da su ne’ya’yan Allah.
15 For you did not receive the spirit of bondage again to fear, but you received the Spirit of adoption, by whom we cry, “Abba! Father!”
Gama ba ku karɓi ruhun da ya mai da ku bayi da za ku sāke jin tsoro ba ne, sai dai kun karɓi Ruhun zaman ɗa. Ta wurinsa kuwa muke kira, “Abba, Uba.”
16 The Spirit himself testifies with our spirit that we are children of God;
Ruhu kansa yana ba da shaida tare da ruhunmu cewa mu’ya’yan Allah ne.
17 and if children, then heirs—heirs of God and joint heirs with Christ, if indeed we suffer with him, that we may also be glorified with him.
In kuwa mu’ya’ya ne, to, mu magāda ne, magādan Allah da kuma abokan gādo tare da Kiristi, in kuwa muna tarayya a cikin shan wuyarsa to, za mu yi tarayya a cikin ɗaukakarsa.
18 For I consider that the sufferings of this present time are not worthy to be compared with the glory which will be revealed toward us.
A ganina, wuyar da muke sha a wannan lokaci ba su isa a kwatanta da ɗaukakar da za a bayyana a cikinmu ba.
19 For the creation waits with eager expectation for the children of God to be revealed.
Halitta tana jira da marmari ta ƙosa ta ga bayyanuwar’ya’yan Allah.
20 For the creation was subjected to vanity, not of its own will, but because of him who subjected it, in hope
Gama an sa halitta a cikin wulaƙanci, ba da son ta ba, sai dai ta wurin nufin wannan da ya mai da ita haka, da bege
21 that the creation itself also will be delivered from the bondage of decay into the liberty of the glory of the children of God.
cewa za a’yantar da halitta kanta daga bautarta ga ruɓewa a kuma kawo ta cikin’yancin ɗaukakar’ya’yan Allah.
22 For we know that the whole creation groans and travails in pain together until now.
Mun san cewa dukan halitta tana nishi sai ka ce mace mai naƙuda har yă zuwa wannan lokaci.
23 Not only so, but ourselves also, who have the first fruits of the Spirit, even we ourselves groan within ourselves, waiting for adoption, the redemption of our body.
Ba haka kaɗai ba ma, mu kanmu da muke da nunan fari na Ruhu, muna nishi a ciki-cikinmu yayinda muke jira da marmari a maishe mu’ya’yan riƙo na Allah, fansar jikunanmu.
24 For we were saved in hope, but hope that is seen is not hope. For who hopes for that which he sees?
Gama a wannan begen ne muka sami ceto. Amma begen da ake gani ba bege ba ne sam. Wa yake begen abin da ya riga ya samu?
25 But if we hope for that which we do not see, we wait for it with patience.
Amma in muna begen abin da ba mu riga mun samu tukuna ba, mukan jira da haƙuri.
26 In the same way, the Spirit also helps our weaknesses, for we do not know how to pray as we ought. But the Spirit himself makes intercession for us with groanings which cannot be uttered.
Haka nan ma, Ruhu yana taimakonmu cikin rashin ƙarfinmu. Ba mu san abin da ya kamata mu roƙa cikin addu’a ba, amma Ruhu kansa yana roƙo a madadinmu da nishe-nishen da kalmomi ba sa iya bayyanawa.
27 He who searches the hearts knows what is on the Spirit’s mind, because he makes intercession for the saints according to God.
Shi kuma wanda yake binciken zukatanmu ya san halin Ruhu, domin Ruhu yana roƙo a madadin tsarkaka bisa ga nufin Allah.
28 We know that all things work together for good for those who love God, for those who are called according to his purpose.
Mun kuma san cewa a cikin dukan abubuwa Allah yana aikata alheri ga waɗanda suke ƙaunarsa, yana waɗanda aka kira bisa ga nufinsa.
29 For whom he foreknew, he also predestined to be conformed to the image of his Son, that he might be the firstborn among many brothers.
Gama waɗanda Allah ya rigyasani ya kuma ƙaddara su dace da kamannin Ɗansa, don yă zama ɗan fari cikin’yan’uwa masu yawa.
30 Whom he predestined, those he also called. Whom he called, those he also justified. Whom he justified, those he also glorified.
Waɗanda kuwa ya ƙaddara, su ne ya kira; waɗanda ya kira kuwa, su ne ya kuɓutar; waɗanda ya kuɓutar kuwa, su ne ya ɗaukaka.
31 What then shall we say about these things? If God is for us, who can be against us?
Me za mu ce ke nan game da wannan abu? In Allah yana goyon bayanmu, wa kuwa zai iya gāba da mu?
32 He who did not spare his own Son, but delivered him up for us all, how would he not also with him freely give us all things?
Shi da bai hana Ɗansa ba, sai ma ya ba da shi saboda mu duka, ashe, ba zai kuma ba mu, tare da shi, dukan abubuwa cikin alherinsa ba?
33 Who could bring a charge against God’s chosen ones? It is God who justifies.
Wa zai kawo wani zargi a kan waɗanda Allah ya zaɓa? Allah ne mai kuɓutarwa.
34 Who is he who condemns? It is Christ who died, yes rather, who was raised from the dead, who is at the right hand of God, who also makes intercession for us.
Wa zai yi hukunci? Yesu Kiristi ne, wanda ya mutu, fiye da haka ma, shi da aka tā da zuwa rai, yana zaune a hannun dama na Allah yana kuma yin roƙo a madadinmu.
35 Who shall separate us from the love of Christ? Could oppression, or anguish, or persecution, or famine, or nakedness, or peril, or sword?
Wane ne zai raba mu da ƙaunar Kiristi? Masifa ce ko wahala ko tsanani ko yunwa ko tsiraici ko hatsari ko takobi?
36 Even as it is written, “For your sake we are killed all day long. We were accounted as sheep for the slaughter.”
Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Saboda kai ne muke fuskantar mutuwa dukan yini; an ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.”
37 No, in all these things we are more than conquerors through him who loved us.
A’a, cikin dukan waɗannan abubuwa mun ma fi masu nasara ta wurin shi wanda ya ƙaunace mu.
38 For I am persuaded that neither death, nor life, nor angels, nor principalities, nor things present, nor things to come, nor powers,
Gama na tabbata cewa ko mutuwa ko rai, ko mala’iku ko aljanu, ko abubuwa na yanzu ko abubuwa masu zuwa nan gaba, ko ikoki,
39 nor height, nor depth, nor any other created thing will be able to separate us from God’s love which is in Christ Jesus our Lord.
ko tsayi ko zurfi, ko wani abu dabam cikin dukan halitta da zai iya raba mu da ƙaunar Allah wadda take cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu.

< Romans 8 >