< Psalms 83 >

1 A song. A Psalm by Asaph. God, do not keep silent. Do not keep silent, and do not be still, God.
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 For, behold, your enemies are stirred up. Those who hate you have lifted up their heads.
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 They conspire with cunning against your people. They plot against your cherished ones.
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 “Come,” they say, “let’s destroy them as a nation, that the name of Israel may be remembered no more.”
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 For they have conspired together with one mind. They form an alliance against you.
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 The tents of Edom and the Ishmaelites; Moab, and the Hagrites;
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 Gebal, Ammon, and Amalek; Philistia with the inhabitants of Tyre;
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 Assyria also is joined with them. They have helped the children of Lot. (Selah)
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Do to them as you did to Midian, as to Sisera, as to Jabin, at the river Kishon;
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 who perished at Endor, who became as dung for the earth.
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 Make their nobles like Oreb and Zeeb, yes, all their princes like Zebah and Zalmunna,
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 who said, “Let’s take possession of God’s pasture lands.”
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 My God, make them like tumbleweed, like chaff before the wind.
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 As the fire that burns the forest, as the flame that sets the mountains on fire,
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 so pursue them with your tempest, and terrify them with your storm.
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 Fill their faces with confusion, that they may seek your name, LORD.
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 Let them be disappointed and dismayed forever. Yes, let them be confounded and perish;
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 that they may know that you alone, whose name is the LORD, are the Most High over all the earth.
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.

< Psalms 83 >