< Psalms 75 >

1 For the Chief Musician. To the tune of “Do Not Destroy.” A Psalm by Asaph. A song. We give thanks to you, God. We give thanks, for your Name is near. Men tell about your wondrous works.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
2 When I choose the appointed time, I will judge blamelessly.
Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
3 The earth and all its inhabitants quake. I firmly hold its pillars. (Selah)
Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
4 I said to the arrogant, “Do not boast!” I said to the wicked, “Do not lift up the horn.
Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
5 Do not lift up your horn on high. Do not speak with a stiff neck.”
Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
6 For neither from the east, nor from the west, nor yet from the south, comes exaltation.
Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
7 But God is the judge. He puts down one, and lifts up another.
Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
8 For in the LORD’s hand there is a cup, full of foaming wine mixed with spices. He pours it out. Indeed the wicked of the earth drink and drink it to its very dregs.
A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
9 But I will declare this forever: I will sing praises to the God of Jacob.
Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
10 I will cut off all the horns of the wicked, but the horns of the righteous shall be lifted up.
wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”

< Psalms 75 >