< Psalms 15 >

1 A Psalm by David. LORD, who shall dwell in your sanctuary? Who shall live on your holy hill?
Zabura ta Dawuda. Ubangiji, wa zai zauna cikin wuri mai tsarkinka? Wa zai zauna a kan tudunka mai tsarki?
2 He who walks blamelessly and does what is right, and speaks truth in his heart;
Sai wanda ba shi da laifi kuma yana yin abin da yake daidai, wanda yake faɗin gaskiya daga zuciyarsa
3 he who does not slander with his tongue, nor does evil to his friend, nor casts slurs against his fellow man;
ba ya kuwa ɓata sunan wani da harshensa, wanda ba ya yi wa maƙwabcinsa mugunta ba ya kuwa baza jita-jita a kan ɗan’uwansa,
4 in whose eyes a vile man is despised, but who honors those who fear the LORD; he who keeps an oath even when it hurts, and does not change;
wanda yake ƙin mugun mutum amma yakan girmama masu tsoron Ubangiji, yakan cika alkawarinsa ko da ma ya zafe shi,
5 he who does not lend out his money for usury, nor take a bribe against the innocent. He who does these things shall never be shaken.
wanda yake ba da rance ba tare da ruwa ba kuma ba ya karɓan cin hanci don yă kā da marar laifi. Shi wanda yake yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa jijjiguwa ba.

< Psalms 15 >