< Psalms 135 >

1 Praise the LORD! Praise the LORD’s name! Praise him, you servants of the LORD,
Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
2 you who stand in the LORD’s house, in the courts of our God’s house.
ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
3 Praise the LORD, for the LORD is good. Sing praises to his name, for that is pleasant.
Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
4 For the LORD has chosen Jacob for himself, Israel for his own possession.
Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
5 For I know that the LORD is great, that our Lord is above all gods.
Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
6 Whatever the LORD pleased, that he has done, in heaven and in earth, in the seas and in all deeps.
Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
7 He causes the clouds to rise from the ends of the earth. He makes lightnings with the rain. He brings the wind out of his treasuries.
Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
8 He struck the firstborn of Egypt, both of man and animal.
Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
9 He sent signs and wonders into the middle of you, Egypt, on Pharaoh, and on all his servants.
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
10 He struck many nations, and killed mighty kings—
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
11 Sihon king of the Amorites, Og king of Bashan, and all the kingdoms of Canaan—
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
12 and gave their land for a heritage, a heritage to Israel, his people.
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
13 Your name, LORD, endures forever; your renown, LORD, throughout all generations.
Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
14 For the LORD will judge his people and have compassion on his servants.
Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
15 The idols of the nations are silver and gold, the work of men’s hands.
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
16 They have mouths, but they cannot speak. They have eyes, but they cannot see.
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
17 They have ears, but they cannot hear, neither is there any breath in their mouths.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
18 Those who make them will be like them, yes, everyone who trusts in them.
Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
19 House of Israel, praise the LORD! House of Aaron, praise the LORD!
Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
20 House of Levi, praise the LORD! You who fear the LORD, praise the LORD!
Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
21 Blessed be the LORD from Zion, who dwells in Jerusalem. Praise the LORD!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.

< Psalms 135 >