< Psalms 118 >

1 Give thanks to the LORD, for he is good, for his loving kindness endures forever.
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Let Israel now say that his loving kindness endures forever.
Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
3 Let the house of Aaron now say that his loving kindness endures forever.
Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
4 Now let those who fear the LORD say that his loving kindness endures forever.
Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
5 Out of my distress, I called on the LORD. The LORD answered me with freedom.
Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
6 The LORD is on my side. I will not be afraid. What can man do to me?
Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
7 The LORD is on my side among those who help me. Therefore I will look in triumph at those who hate me.
Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
8 It is better to take refuge in the LORD, than to put confidence in man.
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
9 It is better to take refuge in the LORD, than to put confidence in princes.
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
10 All the nations surrounded me, but in the LORD’s name I cut them off.
Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
11 They surrounded me, yes, they surrounded me. In the LORD’s name I indeed cut them off.
Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
12 They surrounded me like bees. They are quenched like the burning thorns. In the LORD’s name I cut them off.
Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
13 You pushed me back hard, to make me fall, but the LORD helped me.
An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
14 The LORD is my strength and song. He has become my salvation.
Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
15 The voice of rejoicing and salvation is in the tents of the righteous. “The right hand of the LORD does valiantly.
Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
16 The right hand of the LORD is exalted! The right hand of the LORD does valiantly!”
An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
17 I will not die, but live, and declare the LORD’s works.
Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
18 The LORD has punished me severely, but he has not given me over to death.
Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
19 Open to me the gates of righteousness. I will enter into them. I will give thanks to the LORD.
Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
20 This is the gate of the LORD; the righteous will enter into it.
Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
21 I will give thanks to you, for you have answered me, and have become my salvation.
Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
22 The stone which the builders rejected has become the cornerstone.
Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
23 This is the LORD’s doing. It is marvelous in our eyes.
Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
24 This is the day that the LORD has made. We will rejoice and be glad in it!
Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
25 Save us now, we beg you, LORD! LORD, we beg you, send prosperity now.
Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
26 Blessed is he who comes in the LORD’s name! We have blessed you out of the LORD’s house.
Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
27 The LORD is God, and he has given us light. Bind the sacrifice with cords, even to the horns of the altar.
Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
28 You are my God, and I will give thanks to you. You are my God, I will exalt you.
Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
29 Oh give thanks to the LORD, for he is good, for his loving kindness endures forever.
Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.

< Psalms 118 >