< Psalms 107 >

1 Give thanks to the LORD, for he is good, for his loving kindness endures forever.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Let the redeemed by the LORD say so, whom he has redeemed from the hand of the adversary,
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 and gathered out of the lands, from the east and from the west, from the north and from the south.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 They wandered in the wilderness in a desert way. They found no city to live in.
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 Hungry and thirsty, their soul fainted in them.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Then they cried to the LORD in their trouble, and he delivered them out of their distresses.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 He led them also by a straight way, that they might go to a city to live in.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Let them praise the LORD for his loving kindness, for his wonderful deeds to the children of men!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 For he satisfies the longing soul. He fills the hungry soul with good.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Some sat in darkness and in the shadow of death, being bound in affliction and iron,
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 because they rebelled against the words of God, and condemned the counsel of the Most High.
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 Therefore he brought down their heart with labor. They fell down, and there was no one to help.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Then they cried to the LORD in their trouble, and he saved them out of their distresses.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 He brought them out of darkness and the shadow of death, and broke away their chains.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Let them praise the LORD for his loving kindness, for his wonderful deeds to the children of men!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 For he has broken the gates of bronze, and cut through bars of iron.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Fools are afflicted because of their disobedience, and because of their iniquities.
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 Their soul abhors all kinds of food. They draw near to the gates of death.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Then they cry to the LORD in their trouble, and he saves them out of their distresses.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 He sends his word, and heals them, and delivers them from their graves.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Let them praise the LORD for his loving kindness, for his wonderful deeds to the children of men!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 Let them offer the sacrifices of thanksgiving, and declare his deeds with singing.
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Those who go down to the sea in ships, who do business in great waters,
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 these see the LORD’s deeds, and his wonders in the deep.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 For he commands, and raises the stormy wind, which lifts up its waves.
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 They mount up to the sky; they go down again to the depths. Their soul melts away because of trouble.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 They reel back and forth, and stagger like a drunken man, and are at their wits’ end.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Then they cry to the LORD in their trouble, and he brings them out of their distress.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 He makes the storm a calm, so that its waves are still.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Then they are glad because it is calm, so he brings them to their desired haven.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Let them praise the LORD for his loving kindness, for his wonderful deeds for the children of men!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Let them exalt him also in the assembly of the people, and praise him in the seat of the elders.
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 He turns rivers into a desert, water springs into a thirsty ground,
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 and a fruitful land into a salt waste, for the wickedness of those who dwell in it.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 He turns a desert into a pool of water, and a dry land into water springs.
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 There he makes the hungry live, that they may prepare a city to live in,
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 sow fields, plant vineyards, and reap the fruits of increase.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 He blesses them also, so that they are multiplied greatly. He does not allow their livestock to decrease.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Again, they are diminished and bowed down through oppression, trouble, and sorrow.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 He pours contempt on princes, and causes them to wander in a trackless waste.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 Yet he lifts the needy out of their affliction, and increases their families like a flock.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 The upright will see it, and be glad. All the wicked will shut their mouths.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Whoever is wise will pay attention to these things. They will consider the loving kindnesses of the LORD.
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Psalms 107 >