< Matthew 7 >

1 “Do not judge, so that you will not be judged.
Kada ku yi hukunci, domin ku ma kada a hukunta ku. Domin da irin hukuncin da ku kan hukunta da shi za a hukunta ku.
2 For with whatever judgment you judge, you will be judged; and with whatever measure you measure, it will be measured to you.
Mudun da kukan auna, da shi za a auna maku.
3 Why do you see the speck that is in your brother’s eye, but do not consider the beam that is in your own eye?
Don me kake duban dan hakin da ke idon dan'uwanka, amma ba ka kula da gungumen da ke naka idon ba?
4 Or how will you tell your brother, ‘Let me remove the speck from your eye,’ and behold, the beam is in your own eye?
Ko kuwa yaya za ka iya ce wa dan'uwanka, 'Bari in cire maka dan hakin da ke idon ka,' alhali ga gungume a cikin naka idon?
5 You hypocrite! First remove the beam out of your own eye, and then you can see clearly to remove the speck out of your brother’s eye.
Kai munafiki! Ka fara cire gungumen da ke idonka, sa'annan za ka iya gani sosai yadda za ka cire dan hakin da ke idon dan'uwanka.
6 “Do not give that which is holy to the dogs, neither throw your pearls before the pigs, lest perhaps they trample them under their feet, and turn and tear you to pieces.
Kada ku ba karnuka abin da ke tsattsarka. Kada kuma ku jefa wa aladu, lu'u lu'anku. Idan ba haka ba za su tattake su a karkashin sawunsu, su kuma juyo su kekketa ku.
7 “Ask, and it will be given you. Seek, and you will find. Knock, and it will be opened for you.
Roka, kuma za a ba ku. Nema, kuma za ku samu. Kwankwasa kuma za a bude maku.
8 For everyone who asks receives. He who seeks finds. To him who knocks it will be opened.
Ai duk wanda ya roka, zai karba, kuma duk wanda ya nema zai samu, wanda ya kwankwasa kuma za a bude masa.
9 Or who is there among you who, if his son asks him for bread, will give him a stone?
Ko, kuwa wane mutum ne a cikin ku, dan sa zai roke shi gurasa, ya ba shi dutse?
10 Or if he asks for a fish, who will give him a serpent?
Ko kuwa in ya roke shi kifi, zai ba shi maciji?
11 If you then, being evil, know how to give good gifts to your children, how much more will your Father who is in heaven give good things to those who ask him!
Saboda haka, idan ku da ku ke miyagu, kun san yadda za ku ba da kyautai masu kyau ga 'ya'yanku, ina kimanin yadda Ubanku na sama zai ba da abubuwa masu kyau ga duk wadanda suke rokon sa?
12 Therefore, whatever you desire for men to do to you, you shall also do to them; for this is the law and the prophets.
Saboda haka, duk abinda ku ke so mutane su yi maku, ku ma sai ku yi masu, domin wannan shi ne dukan shari'a da koyarwar annabawa.
13 “Enter in by the narrow gate; for the gate is wide and the way is broad that leads to destruction, and there are many who enter in by it.
Ku shiga ta matsattsiyar kofa, don kofar zuwa hallaka na da fadi, hanyar ta mai saukin bi ce, masu shiga ta cikin ta suna da yawa.
14 How narrow is the gate and the way is restricted that leads to life! There are few who find it.
Domin kofar zuwa rai matsattsiya ce, hanyar ta mai wuyar bi ce, masu samun ta kuwa kadan ne.
15 “Beware of false prophets, who come to you in sheep’s clothing, but inwardly are ravening wolves.
Ku kula da annabawan karya, wadanda su kan zo maku da siffar tumaki, amma a gaskiya kyarketai ne masu warwashewa.
16 By their fruits you will know them. Do you gather grapes from thorns or figs from thistles?
Za ku gane su ta irin ''ya'yansu. Mutane na cirar inabi a jikin kaya, ko kuwa baure a jikin sarkakkiya?
17 Even so, every good tree produces good fruit, but the corrupt tree produces evil fruit.
Haka kowanne itace mai kyau yakan haifi kyawawan 'ya'ya, amma mummunan itace kuwa yakan haifi munanan 'ya'ya.
18 A good tree cannot produce evil fruit, neither can a corrupt tree produce good fruit.
Kyakkyawan itace ba zai taba haifar da munanan 'ya'ya ba, haka kuma mummunan itace ba zai taba haifar da kyawawan 'ya'ya ba.
19 Every tree that does not grow good fruit is cut down and thrown into the fire.
Duk itacen da ba ya ba da 'ya'ya masu kyau, sai a sare shi a jefa a wuta.
20 Therefore by their fruits you will know them.
Domin haka, ta irin 'ya'yansu za a gane su.
21 “Not everyone who says to me, ‘Lord, Lord,’ will enter into the Kingdom of Heaven, but he who does the will of my Father who is in heaven.
Ba duk mai ce mani, 'Ubangiji, Ubangiji,' ne, zai shiga mulkin sama ba, sai dai wanda ya yi nufin Ubana da yake cikin sama.
22 Many will tell me in that day, ‘Lord, Lord, did not we prophesy in your name, in your name cast out demons, and in your name do many mighty works?’
A ranar nan da yawa za su ce mani, 'Ubangiji, Ubangiji,' ashe ba mu yi annabci da sunanka ba, ba mu fitar da aljanu da sunanka ba, ba mu kuma yi manyan ayyuka masu yawa da sunanka ba?'
23 Then I will tell them, ‘I never knew you. Depart from me, you who work iniquity.’
Sa'annan zan ce masu 'Ni ban taba saninku ba! Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta!'
24 “Everyone therefore who hears these words of mine and does them, I will liken him to a wise man who built his house on a rock.
Saboda haka, dukan wanda yake jin maganata, yake kuma aikata ta, za a kwatanta shi da mutum mai hikima, wanda ya gina gidan sa a bisa dutse.
25 The rain came down, the floods came, and the winds blew and beat on that house; and it did not fall, for it was founded on the rock.
Da ruwa ya sauko, ambaliyar ruwa ta zo, iska ta taso ta buga gidan, amma bai fadi ba, domin an gina shi bisa dutse.
26 Everyone who hears these words of mine and does not do them will be like a foolish man who built his house on the sand.
Amma duk wanda ya ji maganar nan tawa, bai aikata ta ba, za a misalta shi da wawan mutum da ya gina gidansa a kan rairayi.
27 The rain came down, the floods came, and the winds blew and beat on that house; and it fell—and its fall was great.”
Ruwa ya sauko, ambaliyar ruwa ta zo, sai iska ta taso ta buga gidan. Sai kuma ya rushe, ya kuwa yi cikakkiyar ragargajewa.''
28 When Jesus had finished saying these things, the multitudes were astonished at his teaching,
Ya zama sa'adda Yesu ya gama fadin wadannan maganganu, sai taro suka yi mamakin koyarwarsa,
29 for he taught them with authority, and not like the scribes.
Domin yana koya masu da iko, ba kamar marubuta ba.

< Matthew 7 >