< Matthew 7 >

1 “Do not judge, so that you will not be judged.
“Kada ku ba wa kowa laifi, don kada a ba ku laifi ku ma.
2 For with whatever judgment you judge, you will be judged; and with whatever measure you measure, it will be measured to you.
Gama da irin shari’ar da kuka yi wa waɗansu, da ita za a shari’anta ku. Mudun da kuka yi awo da shi, da shi za a yi muku.
3 Why do you see the speck that is in your brother’s eye, but do not consider the beam that is in your own eye?
“Don me kake duban ɗan tsinken da yake idon ɗan’uwanka, alhali kuwa ga gungume a naka ido?
4 Or how will you tell your brother, ‘Let me remove the speck from your eye,’ and behold, the beam is in your own eye?
Yaya za ka ce wa ɗan’uwanka, ‘Bari in cire maka ɗan tsinken nan daga idonka,’ alhali kuwa a kowane lokaci akwai gungume a naka ido?
5 You hypocrite! First remove the beam out of your own eye, and then you can see clearly to remove the speck out of your brother’s eye.
Kai munafuki, fara cire gungumen da yake idonka, a sa’an nan ne za ka iya gani sosai yadda za ka cire ɗan tsinken da yake a idon ɗan’uwanka.
6 “Do not give that which is holy to the dogs, neither throw your pearls before the pigs, lest perhaps they trample them under their feet, and turn and tear you to pieces.
“Kada ku ba karnuka abin da yake mai tsarki; kada kuma ku jefa wa aladu lu’ulu’anku. In kuka yi haka za su tattake su, sa’an nan su juyo su jijji muku ciwo.
7 “Ask, and it will be given you. Seek, and you will find. Knock, and it will be opened for you.
“Ku roƙa za a ba ku; ku nema za ku samu; ku ƙwanƙwasa za a kuwa buɗe muku ƙofa.
8 For everyone who asks receives. He who seeks finds. To him who knocks it will be opened.
Gama duk wanda ya roƙa, akan ba shi; wanda ya nema kuwa, yakan samu, wanda kuma ya ƙwanƙwasa, za a buɗe masa ƙofa.
9 Or who is there among you who, if his son asks him for bread, will give him a stone?
“Wane ne a cikinku in ɗansa ya roƙe shi burodi, sai yă ba shi dutse?
10 Or if he asks for a fish, who will give him a serpent?
Ko kuwa in ya roƙe shi kifi, sai yă ba shi maciji?
11 If you then, being evil, know how to give good gifts to your children, how much more will your Father who is in heaven give good things to those who ask him!
In ku da kuke mugaye kun san yadda za ku ba da kyautai masu kyau ga’ya’yanku, balle Ubanku na sama, ba zai fi ku iya ba da abubuwa masu kyau, ga su waɗanda suka roƙe shi ba!
12 Therefore, whatever you desire for men to do to you, you shall also do to them; for this is the law and the prophets.
Saboda haka, duk abin da kuke so mutane su yi muku, ku ma sai ku yi musu, domin wannan shi ne Doka da koyarwar Annabawa sun ƙunsa.
13 “Enter in by the narrow gate; for the gate is wide and the way is broad that leads to destruction, and there are many who enter in by it.
“Ku shiga ta matsattsiyar ƙofa. Gama ƙofar zuwa hallaka faɗaɗɗiya ce mai sauƙin bi kuma, masu shiga ta cikinta kuwa suna da yawa.
14 How narrow is the gate and the way is restricted that leads to life! There are few who find it.
Amma ƙofar zuwa rai, ƙarama ce matsattsiya kuma, masu samunta kuwa kaɗan ne.
15 “Beware of false prophets, who come to you in sheep’s clothing, but inwardly are ravening wolves.
“Ku yi hankali da annabawan ƙarya. Sukan zo muku da kamannin tumaki, amma daga ciki mugayen kyarketai ne.
16 By their fruits you will know them. Do you gather grapes from thorns or figs from thistles?
Ta wurin aikinsu za ku gane su. Mutane suna iya tsinkan inabi a jikin ƙaya, ko kuwa ɓaure a jikin sarƙaƙƙiya?
17 Even so, every good tree produces good fruit, but the corrupt tree produces evil fruit.
Haka ma kowane itace mai kyau yakan ba da’ya’ya masu kyau, kuma mummunan itace ba ya ba da’ya’ya masu kyau.
18 A good tree cannot produce evil fruit, neither can a corrupt tree produce good fruit.
Itace mai kyau ba ya ba da munanan’ya’ya, haka kuma mummunan itace ba ya ba da’ya’ya masu kyau.
19 Every tree that does not grow good fruit is cut down and thrown into the fire.
Duk itacen da ba ya ba da’ya’ya masu kyau sai a sare shi a jefa cikin wuta.
20 Therefore by their fruits you will know them.
Ta haka, ta wurin aikinsu za ku gane su.”
21 “Not everyone who says to me, ‘Lord, Lord,’ will enter into the Kingdom of Heaven, but he who does the will of my Father who is in heaven.
“Ba duk mai ce mini, ‘Ubangiji, Ubangiji,’ ne zai shiga mulkin sama ba, sai dai wanda yake aikata nufin Ubana da yake sama.
22 Many will tell me in that day, ‘Lord, Lord, did not we prophesy in your name, in your name cast out demons, and in your name do many mighty works?’
Da yawa za su ce mini a wannan rana, ‘Ubangiji, Ubangiji, ashe, ba mu yi annabci a cikin sunanka ba, ba kuma a cikin sunanka ne muka fitar da aljanu, muka yi abubuwan banmamaki da yawa ba?’
23 Then I will tell them, ‘I never knew you. Depart from me, you who work iniquity.’
Sa’an nan zan ce musu a fili, ‘Ban taɓa saninku ba. Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta!’
24 “Everyone therefore who hears these words of mine and does them, I will liken him to a wise man who built his house on a rock.
“Saboda haka duk wanda yake jin kalmomin nan nawa yake kuma aikata su, yana kama da mutum mai hikima wanda ya gina gidansa a kan dutse.
25 The rain came down, the floods came, and the winds blew and beat on that house; and it did not fall, for it was founded on the rock.
Ruwan sama ya sauko, rafuffuka suka cika, iska kuma ta hura ta bugi gidan; duk da haka bai fāɗi ba, gama yana da harsashinsa a kan dutse.
26 Everyone who hears these words of mine and does not do them will be like a foolish man who built his house on the sand.
Amma duk wanda yake jin kalmomin nan nawa bai kuwa aikata su ba, yana kama da wani wawa wanda ya gina gidansa a kan yashi.
27 The rain came down, the floods came, and the winds blew and beat on that house; and it fell—and its fall was great.”
Ruwan sama ya sauko, rafuffuka suka cika, iska kuwa ta hura ta bugi gidan, sai ya fāɗi da mummunar ragargajewa kuwa.”
28 When Jesus had finished saying these things, the multitudes were astonished at his teaching,
Sa’ad da Yesu ya gama faɗin waɗannan abubuwa, sai taron mutanen suka yi mamakin koyarwarsa,
29 for he taught them with authority, and not like the scribes.
domin ya koyar kamar wani wanda yake da iko, ba kamar malamansu na dokoki ba.

< Matthew 7 >