< Matthew 6 >

1 “Be careful that you do not do your charitable giving before men, to be seen by them, or else you have no reward from your Father who is in heaven.
“Ku yi hankali kada ku nuna ‘ayyukanku na adalci’ a gaban mutane, don su gani. In kuka yi haka, ba za ku sami lada daga wurin Ubanku da yake cikin sama ba.
2 Therefore, when you do merciful deeds, do not sound a trumpet before yourself, as the hypocrites do in the synagogues and in the streets, that they may get glory from men. Most certainly I tell you, they have received their reward.
“Saboda haka sa’ad da kake ba wa masu bukata taimako, kada ka yi shelarsa, yadda munafukai suke yi a majami’u da kuma kan tituna, don mutane su yabe su. Gaskiya nake gaya muku, sun riga sun sami ladarsu cikakke.
3 But when you do merciful deeds, do not let your left hand know what your right hand does,
Amma sa’ad da kake ba wa masu bukata taimako, kada ka yarda hannun hagunka yă ma san abin da hannun damarka yake yi,
4 so that your merciful deeds may be in secret, then your Father who sees in secret will reward you openly.
don bayarwarka ta zama a ɓoye. Ubanka kuwa mai ganin abin da ake yi a ɓoye, zai sāka maka.
5 “When you pray, you shall not be as the hypocrites, for they love to stand and pray in the synagogues and in the corners of the streets, that they may be seen by men. Most certainly, I tell you, they have received their reward.
“Sa’ad da kuma kuke addu’a, kada ku zama kamar munafukai, gama sun cika son yin addu’a a tsaye a cikin majami’u da kuma a bakin titi, don mutane su gan su. Gaskiya nake gaya muku, sun riga sun sami ladarsu cikakke.
6 But you, when you pray, enter into your inner room, and having shut your door, pray to your Father who is in secret; and your Father who sees in secret will reward you openly.
Amma sa’ad da kake addu’a, sai ka shiga ɗakinka, ka rufe ƙofa, ka yi addu’a ga Ubanka wanda ba a gani. Ubanka kuwa mai ganin abin da ake yi a ɓoye, zai sāka maka.
7 In praying, do not use vain repetitions as the Gentiles do; for they think that they will be heard for their much speaking.
Sa’ad da kuma kuke addu’a, kada ku yi ta maimaita magana, kamar marasa sanin Allah, domin suna tsammani za a ji su saboda yawan maganarsu.
8 Therefore do not be like them, for your Father knows what things you need before you ask him.
Kada ku zama kamar su, gama Ubanku ya san abin da kuke bukata kafin ma ku roƙe shi.
9 Pray like this: “‘Our Father in heaven, may your name be kept holy.
“To, ga yadda ya kamata ku yi addu’a. “‘Ubanmu wanda yake cikin sama, a tsarkake sunanka,
10 Let your Kingdom come. Let your will be done on earth as it is in heaven.
mulkinka yă zo a aikata nufinka a duniya kamar yadda ake yi a sama.
11 Give us today our daily bread.
Ka ba mu yau abincin yininmu.
12 Forgive us our debts, as we also forgive our debtors.
Ka gafarta mana laifofinmu, kamar yadda mu ma muke gafarta wa masu yin mana laifi.
13 Bring us not into temptation, but deliver us from the evil one.'
Kada ka bari a kai mu cikin jarraba, amma ka cece mu daga mugun nan.’
14 “For if you forgive men their trespasses, your heavenly Father will also forgive you.
Gama in kuna yafe wa mutane sa’ad da suka yi muku laifi, Ubanku da yake cikin sama ma zai gafarta muku.
15 But if you do not forgive men their trespasses, neither will your Father forgive your trespasses.
Amma in ba kwa yafe wa mutane laifofinsu, Ubanku ma ba zai gafarta muku zunubanku ba.
16 “Moreover when you fast, do not be like the hypocrites, with sad faces. For they disfigure their faces that they may be seen by men to be fasting. Most certainly I tell you, they have received their reward.
“Sa’ad da kuma kuna azumi, kada ku ɓata fuska, yadda munafukai suke yi. Sukan ɓata fuskokinsu domin su nuna wa mutane cewa suna azumi. Gaskiya nake gaya muku, sun riga sun sami ladarsu cikakke.
17 But you, when you fast, anoint your head and wash your face,
Amma sa’ad da kana azumi, ka shafa wa kanka mai, ka wanke fuskarka,
18 so that you are not seen by men to be fasting, but by your Father who is in secret; and your Father, who sees in secret, will reward you.
domin kada mutane su ga alama cewa kana azumi, sai dai Ubanka kaɗai wanda ba a gani; Ubanka kuwa mai ganin abin da ake yi a ɓoye, zai sāka maka.
19 “Do not lay up treasures for yourselves on the earth, where moth and rust consume, and where thieves break through and steal;
“Kada ku yi wa kanku ajiyar dukiya a duniya, inda asu da tsatsa suke ɓatawa, inda kuma ɓarayi sukan fasa, su yi sata.
20 but lay up for yourselves treasures in heaven, where neither moth nor rust consume, and where thieves do not break through and steal;
Amma ku yi wa kanku ajiyar dukiya a sama, inda ba tsatsa da asu da za su ɓata su, inda kuma ba ɓarayin da za su fasa, su yi sata.
21 for where your treasure is, there your heart will be also.
Gama inda dukiyarka take, a nan ne fa zuciyarka za tă kasance.
22 “The lamp of the body is the eye. If therefore your eye is sound, your whole body will be full of light.
“Ido shi ne fitilar jiki. In idanunka suna da kyau, dukan jikinka zai cika da haske.
23 But if your eye is evil, your whole body will be full of darkness. If therefore the light that is in you is darkness, how great is the darkness!
Amma in idanunka suna da lahani, dukan jikinka ma zai cika da duhu. To, in hasken da yake a cikinka duhu ne, duhun ya wuce misali ke nan!
24 “No one can serve two masters, for either he will hate the one and love the other, or else he will be devoted to one and despise the other. You cannot serve both God and Mammon.
“Ba mai iya bauta wa iyayengiji biyu. Ko dai yă ƙi ɗaya, yă ƙaunaci ɗaya, ko kuwa yă yi aminci ga ɗaya, sa’an nan yă rena ɗayan. Ba dama ku bauta wa Allah, ku kuma bauta wa kuɗi gaba ɗaya.”
25 Therefore I tell you, do not be anxious for your life: what you will eat, or what you will drink; nor yet for your body, what you will wear. Is not life more than food, and the body more than clothing?
“Saboda haka, ina gaya muku, kada ku damu game da rayuwarku, game da abin da za ku ci, ko abin da za ku sha; ko kuma game da jikinku, game da abin da za ku sa. Ashe, rai bai fi abinci ba, jiki kuma bai fi tufafi ba?
26 See the birds of the sky, that they do not sow, neither do they reap, nor gather into barns. Your heavenly Father feeds them. Are not you of much more value than they?
Ku dubi tsuntsayen sararin sama mana; ba sa shuki ko girbi ko ajiya a rumbuna, duk da haka, Ubanku na sama yana ciyar da su. Ashe, ba ku fi su daraja nesa ba?
27 “Which of you by being anxious, can add one moment to his lifespan?
Wane ne a cikinku ta wurin damuwa zai iya ƙara wa rayuwarsa ko sa’a ɗaya?
28 Why are you anxious about clothing? Consider the lilies of the field, how they grow. They do not toil, neither do they spin,
“Me ya sa kuke damuwa a kan riguna? Ku dubi yadda furannin jeji suke girma mana. Ba sa aiki ko saƙa.
29 yet I tell you that even Solomon in all his glory was not dressed like one of these.
Duk da haka ina gaya muku ko Solomon cikin dukan darajarsa bai sa kayan adon da ya kai na ko ɗaya a cikinsu ba.
30 But if God so clothes the grass of the field, which today exists and tomorrow is thrown into the oven, will not he much more clothe you, you of little faith?
In haka Allah yake yi wa ciyawar jeji sutura, wadda yau tana nan, gobe kuwa a jefa a cikin wuta, ba zai ma fi yi muku sutura ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya?
31 “Therefore do not be anxious, saying, ‘What will we eat?’, ‘What will we drink?’ or, ‘With what will we be clothed?’
Don haka, kada ku damu, kuna cewa, ‘Me za mu ci?’ Ko, ‘Me za mu sha?’ Ko kuma, ‘Me za mu sa?’
32 For the Gentiles seek after all these things; for your heavenly Father knows that you need all these things.
Gama marasa sanin Allah suna fama neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa ya san kuna bukatarsu.
33 But seek first God’s Kingdom and his righteousness; and all these things will be given to you as well.
Da farko dai, ku nemi mulkin Allah da kuma adalcinsa, za a kuwa ba ku dukan waɗannan abubuwa.
34 Therefore do not be anxious for tomorrow, for tomorrow will be anxious for itself. Each day’s own evil is sufficient.
Saboda haka kada ku damu game da gobe, gama gobe zai damu da kansa. Damuwar yau ma ta isa wahala.

< Matthew 6 >