< Mark 13 >

1 As he went out of the temple, one of his disciples said to him, “Teacher, see what kind of stones and what kind of buildings!”
Da yake barin haikalin, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Malam! Dubi irin manya-manyan duwatsun nan! Ka ga irin gine-ginen nan masu kyau mana!”
2 Jesus said to him, “Do you see these great buildings? There will not be left here one stone on another, which will not be thrown down.”
Yesu ya amsa ya ce, “Ka ga dukan manyan gine-ginen nan? Ba wani dutse a nan, da za a bari kan wani da ba za a rushe ba.”
3 As he sat on the Mount of Olives opposite the temple, Peter, James, John, and Andrew asked him privately,
Da Yesu yana zaune a kan Dutsen Zaitun da yake ɗaura da haikali, sai Bitrus, Yaƙub, Yohanna da kuma Andarawus, suka tambaye shi a ɓoye, suka ce,
4 “Tell us, when will these things be? What is the sign that these things are all about to be fulfilled?”
“Ka gaya mana, yaushe waɗannan abubuwa za su faru? Wace alama ce kuma za tă nuna cewa, duk waɗannan suna dab da cikawa?”
5 Jesus, answering, began to tell them, “Be careful that no one leads you astray.
Sai Yesu ya ce musu, “Ku lura fa kada wani yă ruɗe ku.
6 For many will come in my name, saying, ‘I am he!’ and will lead many astray.
Da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne shi.’ Za su kuwa ruɗi mutane da yawa.
7 “When you hear of wars and rumors of wars, do not be troubled. For those must happen, but the end is not yet.
Sa’ad da kuka ji labarun yaƙe-yaƙe da jita-jitar yaƙe-yaƙe, kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru. Amma ƙarshen tukuna.
8 For nation will rise against nation, and kingdom against kingdom. There will be earthquakes in various places. There will be famines and troubles. These things are the beginning of birth pains.
Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki kuma yă tasar wa mulki. Za a yi girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam, a kuma yi yunwa. Waɗannan dai mafarin azabar naƙuda.
9 “But watch yourselves, for they will deliver you up to councils. You will be beaten in synagogues. You will stand before rulers and kings for my sake, for a testimony to them.
“Dole ku yi zaman tsaro. Za a ba da ku ga hukuma, a kuma bulale ku a majami’u. Saboda ni kuma, za ku tsaya a gaban gwamnoni da sarakuna, domin ku ba da shaida a gabansu.
10 The Good News must first be preached to all the nations.
Dole sai an fara yin wa’azin bishara ga dukan al’ummai.
11 When they lead you away and deliver you up, do not be anxious beforehand or premeditate what you will say, but say whatever will be given you in that hour. For it is not you who speak, but the Holy Spirit.
Sa’ad da aka kama ku, aka kuma kai ku don a yi muku shari’a, kada ku damu da abin da za ku faɗa. Sai dai ku faɗi abin da aka ba ku a lokacin. Gama ba ku kuke magana ba, Ruhu Mai Tsarki ne.
12 “Brother will deliver up brother to death, and the father his child. Children will rise up against parents and cause them to be put to death.
“Ɗan’uwa zai ba da ɗan’uwa a kashe. Mahaifi zai ba da ɗansa.’Ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
13 You will be hated by all men for my name’s sake, but he who endures to the end will be saved.
Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto.
14 “But when you see the abomination of desolation, spoken of by Daniel the prophet, standing where it ought not” (let the reader understand), “then let those who are in Judea flee to the mountains,
“Sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama, mai kawo hallaka’tsaye indabai kamata ba (mai karatu ya gane), to, sai waɗanda suke a Yahudiya su gudu zuwa duwatsu.
15 and let him who is on the housetop not go down, nor enter in, to take anything out of his house.
Kada wani da yake kan rufin gidansa yă sauka, ko yă shiga gida don yă ɗauki wani abu.
16 Let him who is in the field not return back to take his cloak.
Kada wani da yake gona kuma yă koma don ɗaukar rigarsa.
17 But woe to those who are with child and to those who nurse babies in those days!
Kaiton mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya a waɗancan kwanakin!
18 Pray that your flight will not be in the winter.
Ku yi addu’a, kada wannan yă faru a lokacin sanyi.
19 For in those days there will be oppression, such as there has not been the like from the beginning of the creation which God created until now, and never will be.
Domin waɗancan kwanakin za su zama kwanaki na baƙin ciki, waɗanda ba a taɓa yin irinsa ba tun farkon halitta, har yă zuwa yanzu, ba kuwa za a sāke yin irinsa ba.
20 Unless the Lord had shortened the days, no flesh would have been saved; but for the sake of the chosen ones, whom he picked out, he shortened the days.
“Da ba don Ubangiji ya rage kwanakin nan ba, da ba wani da zai tsira. Amma saboda zaɓaɓɓu waɗanda ya zaɓa, sai ya rage kwanakin.
21 Then if anyone tells you, ‘Look, here is the Christ!’ or, ‘Look, there!’ do not believe it.
A lokacin nan, in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko kuwa, ‘Duba, ga shi can!’ Kada ku gaskata.
22 For false christs and false prophets will arise and will show signs and wonders, that they may lead astray, if possible, even the chosen ones.
Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu.
23 But you watch. “Behold, I have told you all things beforehand.
Amma ku kula! Na dai gaya muku kome tun da wuri.
24 But in those days, after that oppression, the sun will be darkened, the moon will not give its light,
“Amma waɗancan kwanaki, bayan baƙin azaban nan, “‘rana za tă yi duhu, wata kuma ba zai ba da haskensa ba;
25 the stars will be falling from the sky, and the powers that are in the heavens will be shaken.
taurari za su fāffāɗo daga sararin sama. Za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama.’
26 Then they will see the Son of Man coming in clouds with great power and glory.
“Sa’an nan, mutane za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin gizagizai da iko, da ɗaukaka mai girma.
27 Then he will send out his angels, and will gather together his chosen ones from the four winds, from the ends of the earth to the ends of the sky.
Zai kuma aiko mala’ikunsa su tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga iyakar duniya har yă zuwa iyakar sama.
28 “Now from the fig tree, learn this parable. When the branch has now become tender and produces its leaves, you know that the summer is near;
“To, sai ku yi koyi da itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi, ganyayensa kuma suka toho, kun san cewa damina ta yi kusa ke nan.
29 even so you also, when you see these things coming to pass, know that it is near, at the doors.
Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku san cewa ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
30 Most certainly I say to you, this generation will not pass away until all these things happen.
Gaskiya nake gaya muku, zamanin nan ba zai shuɗe ba sai duk abubuwan nan sun faru.
31 Heaven and earth will pass away, but my words will not pass away.
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
32 “But of that day or that hour no one knows—not even the angels in heaven, nor the Son, but only the Father.
“Game da wannan rana ko sa’a kuwa, ba wanda ya sani, ko mala’ikun da suke sama, ko Ɗan, sai Uban kaɗai.
33 Watch, keep alert, and pray; for you do not know when the time is.
Ku lura fa! Ku zauna a shirye! Don ba ku san lokacin da shi zai zo ba.
34 “It is like a man traveling to another country, having left his house and given authority to his servants, and to each one his work, and also commanded the doorkeeper to keep watch.
Yana kama da mutumin da zai yi tafiya. Yakan bar gidansa a hannun bayinsa, kowa da nasa aikin da aka sa shi, yă kuma ce wa wanda yake gadin ƙofa, yă yi tsaro.
35 Watch therefore, for you do not know when the lord of the house is coming—whether at evening, or at midnight, or when the rooster crows, or in the morning;
“Saboda haka, sai ku zauna a shirye, domin ba ku san lokacin da maigidan zai dawo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko lokacin da zakara na cara ne, ko kuma da safe ne.
36 lest, coming suddenly, he might find you sleeping.
In ya zo kwaram, kada ka bari yă tarar da kai kana barci.
37 What I tell you, I tell all: Watch!”
Abin da na faɗa muku, na faɗa wa kowa. ‘Ku yi tsaro!’”

< Mark 13 >