< Luke 3 >

1 Now in the fifteenth year of the reign of Tiberius Caesar, Pontius Pilate being governor of Judea, and Herod being tetrarch of Galilee, and his brother Philip tetrarch of the region of Ituraea and Trachonitis, and Lysanias tetrarch of Abilene,
A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Kaisar Tiberiyus, a lokacin Buntus Bilatus ne gwamnar Yahudiya, Hiridus kuma yana sarautar Galili, ɗan’uwansa Filibus yana sarautar Ituriya da Tarakunitis, Lisaniyas kuma yana sarautar Abiline.
2 during the high priesthood of Annas and Caiaphas, the word of God came to John, the son of Zacharias, in the wilderness.
A lokacin ne Annas da Kayifas suke manyan firistoci. Sai maganar Allah ta zo wa Yohanna, ɗan Zakariya a hamada.
3 He came into all the region around the Jordan, preaching the baptism of repentance for remission of sins.
Ya zaga dukan ƙasar da take kewaye da Urdun, yana wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
4 As it is written in the book of the words of Isaiah the prophet, “The voice of one crying in the wilderness, ‘Make ready the way of the Lord. Make his paths straight.
Kamar yadda yake a rubuce a littafin annabi Ishaya. “Muryar mai kira a hamada, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.
5 Every valley will be filled. Every mountain and hill will be brought low. The crooked will become straight, and the rough ways smooth.
Za a cike kowane kwari, a farfashe kowane dutse da kowane tudu. Za a miƙe hanyoyin da suka karkace, a gyaggyara hanyoyi masu gargaɗa su zama sumul.
6 All flesh will see God’s salvation.’”
Dukan’yan Adam kuwa za su ga ceton Allah!’”
7 He said therefore to the multitudes who went out to be baptized by him, “You offspring of vipers, who warned you to flee from the wrath to come?
Yohanna ya ce wa taron da suke zuwa domin yă yi musu baftisma, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku, ku guje wa fushin nan mai zuwa?
8 Therefore produce fruits worthy of repentance, and do not begin to say among yourselves, ‘We have Abraham for our father;’ for I tell you that God is able to raise up children to Abraham from these stones!
Ku yi ayyukan da suka dace da tuba. Kada ma ku yi tunani za ku iya ce wa kanku, ‘Ai, muna da mahaifinmu Ibrahim.’ Ina gaya muku cewa daga cikin duwatsun nan Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim.
9 Even now the ax also lies at the root of the trees. Every tree therefore that does not produce good fruit is cut down and thrown into the fire.”
An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.”
10 The multitudes asked him, “What then must we do?”
Sai taron suka tambaye shi, suka ce “Me za mu yi ke nan?”
11 He answered them, “He who has two coats, let him give to him who has none. He who has food, let him do likewise.”
Ya amsa ya ce, “Ya kamata, mutumin da yake da riguna biyu, yă raba da wanda ba shi da riga, mai abinci kuma yă yi haka.”
12 Tax collectors also came to be baptized, and they said to him, “Teacher, what must we do?”
Masu karɓar haraji ma suka zo, domin a yi musu baftisma. Suka yi tambaya, suka ce “Malam, me ya kamata mu yi?”
13 He said to them, “Collect no more than that which is appointed to you.”
Ya ce musu, “Kada ku karɓa fiye da abin da aka ce a karɓa.”
14 Soldiers also asked him, saying, “What about us? What must we do?” He said to them, “Extort from no one by violence, neither accuse anyone wrongfully. Be content with your wages.”
Sai waɗansu sojoji suka tambaye shi, “Mu fa? Me ya kamata mu yi?” Sai ya amsa ya ce, “Kada ku ƙwace kuɗin mutane, kada kuma ku yi shaidar ƙarya. Ku yi haƙuri da abin da ake biyanku.”
15 As the people were in expectation, and all men reasoned in their hearts concerning John, whether perhaps he was the Christ,
Mutane suka zuba ido, suna kuma tunani a zuciyarsu, ko Yohanna ne Kiristi wanda ake sauraron zuwansa.
16 John answered them all, “I indeed baptize you with water, but he comes who is mightier than I, the strap of whose sandals I am not worthy to loosen. He will baptize you in the Holy Spirit and fire.
Yohanna ya amsa musu duka ya ce, “Ina muku baftisma da ruwa. Amma wani wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban ma isa in kunce igiyar takalmansa ba. Shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da wuta kuma.
17 His winnowing fan is in his hand, and he will thoroughly cleanse his threshing floor, and will gather the wheat into his barn; but he will burn up the chaff with unquenchable fire.”
Matankaɗinsa yana a hannunsa don yă tankaɗe sussukarsa ya kuma tattara alkama cikin rumbunsa, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
18 Then with many other exhortations he preached good news to the people,
Da kalmomi masu yawa Yohanna ya yi wa mutane gargaɗi, ya kuma yi musu wa’azin bishara.
19 but Herod the tetrarch, being reproved by him for Herodias, his brother’s wife, and for all the evil things which Herod had done,
Amma da Yohanna ya tsawata wa Hiridus mai mulki saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa, da kuma dukan sauran mugayen abubuwan da ya yi,
20 added this also to them all, that he shut up John in prison.
Hiridus dai ya ƙara ɓata al’amarin. Ya sa a kulle Yohanna a kurkuku.
21 Now when all the people were baptized, Jesus also had been baptized and was praying. The sky was opened,
Sa’ad da ake wa dukan mutane baftisma, sai aka yi wa Yesu shi ma. Da yana cikin addu’a, sai sama ya buɗe,
22 and the Holy Spirit descended in a bodily form like a dove on him; and a voice came out of the sky, saying “You are my beloved Son. In you I am well pleased.”
Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauko masa a wata siffa, kamar kurciya. Sai murya ta fito daga sama, ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, kai ne kuma kana faranta mini zuciya ƙwarai.”
23 Jesus himself, when he began to teach, was about thirty years old, being the son (as was supposed) of Joseph, the son of Heli,
To, Yesu kansa yana da shekaru kusan talatin da haihuwa sa’ad da ya fara aikinsa. An ɗauka shi ɗan Yusuf ne, ɗan Heli,
24 the son of Matthat, the son of Levi, the son of Melchi, the son of Jannai, the son of Joseph,
ɗan Mattat, ɗan Lawi, ɗan Melki, ɗan Yannai, ɗan Yusuf,
25 the son of Mattathias, the son of Amos, the son of Nahum, the son of Esli, the son of Naggai,
ɗan Mattatiyas, ɗan Amos, ɗan Nahum, ɗan Esli, ɗan Naggai,
26 the son of Maath, the son of Mattathias, the son of Semein, the son of Joseph, the son of Judah,
ɗan Ma’at, ɗan Mattatiyas, ɗan Semeyin, ɗan Yosek, ɗan Yoda,
27 the son of Joanan, the son of Rhesa, the son of Zerubbabel, the son of Shealtiel, the son of Neri,
ɗan Yowanan, ɗan Resa, ɗan Zerubbabel, ɗan Sheyaltiyel, ɗan Neri,
28 the son of Melchi, the son of Addi, the son of Cosam, the son of Elmodam, the son of Er,
ɗan Melki, ɗan Addi, ɗan Kosam, ɗan Elmadam, ɗan Er,
29 the son of Jose, the son of Eliezer, the son of Jorim, the son of Matthat, the son of Levi,
ɗan Yoshuwa, ɗan Eliyezer, ɗan Yorim, ɗan Mattat, ɗan Lawi,
30 the son of Simeon, the son of Judah, the son of Joseph, the son of Jonan, the son of Eliakim,
ɗan Simeyon, ɗan Yahuda, ɗan Yusuf, ɗan Yonam, ɗan Eliyakim,
31 the son of Melea, the son of Menan, the son of Mattatha, the son of Nathan, the son of David,
ɗan Meleya, ɗan Menna, ɗan Mattata, ɗan Natan, ɗan Dawuda,
32 the son of Jesse, the son of Obed, the son of Boaz, the son of Salmon, the son of Nahshon,
ɗan Yesse, ɗan Obed, ɗan Bowaz, ɗan Salmon, ɗan Nashon,
33 the son of Amminadab, the son of Aram, the son of Hezron, the son of Perez, the son of Judah,
ɗan Amminadab, ɗan Ram, ɗan Hezron, ɗan Ferez, ɗan Yahuda,
34 the son of Jacob, the son of Isaac, the son of Abraham, the son of Terah, the son of Nahor,
ɗan Yaƙub, ɗan Ishaku, ɗan Ibrahim, ɗan Tera, ɗan Nahor,
35 the son of Serug, the son of Reu, the son of Peleg, the son of Eber, the son of Shelah,
ɗan Serug, ɗan Reyu, ɗan Feleg, ɗan Eber, ɗan Sala,
36 the son of Cainan, the son of Arphaxad, the son of Shem, the son of Noah, the son of Lamech,
ɗan Kainan, ɗan Arfakshad, ɗan Shem, ɗan Nuhu, ɗan Lamek,
37 the son of Methuselah, the son of Enoch, the son of Jared, the son of Mahalaleel, the son of Cainan,
ɗan Metusela, ɗan Enok, ɗan Yared, ɗan Mahalalel, ɗan Kainan,
38 the son of Enos, the son of Seth, the son of Adam, the son of God.
ɗan Enosh, ɗan Shitu, ɗan Adamu, ɗan Allah.

< Luke 3 >