< John 15 >

1 “I am the true vine, and my Father is the farmer.
“Nine itacen inabi na hakika, Ubana kuwa shi ne manomin.
2 Every branch in me that does not bear fruit, he takes away. Every branch that bears fruit, he prunes, that it may bear more fruit.
Yakan cire duk wani rashe a cikina da ba ya bada 'ya'ya, mai bada 'ya'ya kuwa ya kan gyara shi domin ya kara bada 'ya'ya.
3 You are already pruned clean because of the word which I have spoken to you.
Kun rigaya kun tsarkaka saboda maganar da na yi muku.
4 Remain in me, and I in you. As the branch cannot bear fruit by itself unless it remains in the vine, so neither can you, unless you remain in me.
Ku zauna ciki na, Ni kuma cikin ku. Kamar yadda reshe ba ya iya bada 'ya'ya shi kadai sai ya zauna cikin itacen, haka kuma ba za ku iya ba, sai kun zauna ciki na.
5 I am the vine. You are the branches. He who remains in me and I in him bears much fruit, for apart from me you can do nothing.
Ni ne itacen inabi, ku ne rassan. Wanda ya zauna ciki na, ni kuma cikin sa, yana bada 'ya'ya dayawa, gama in ba tare da ni ba, ba za ku iya yin kome ba.
6 If a man does not remain in me, he is thrown out as a branch and is withered; and they gather them, throw them into the fire, and they are burned.
Wanda kuma bai zauna a ciki na ba, akan jefar da shi kamar reshe, ya bushe, kuma sukan tattara rassan su jefa a wuta, su kone.
7 If you remain in me, and my words remain in you, you will ask whatever you desire, and it will be done for you.
In kun zauna a ciki na, maganata kuma ta zauna a cikin ku, sai ku roki duk abinda kuke so, za a kuwa yi maku.
8 “In this my Father is glorified, that you bear much fruit; and so you will be my disciples.
Ta haka ake daukaka Ubana: cewa ku bada 'ya'ya dayawa, kuma cewa ku almajiraina ne.
9 Even as the Father has loved me, I also have loved you. Remain in my love.
Kamar yadda Ubana ya kaunace ni, haka Ni ma na kaunace ku; Ku zauna cikin kaunata.
10 If you keep my commandments, you will remain in my love, even as I have kept my Father’s commandments and remain in his love.
Idan kun kiyaye dokokina, za ku zauna cikin kaunata kamar yadda Na kiyaye dokokin Ubana, na kuma zauna cikin kaunarsa.
11 I have spoken these things to you, that my joy may remain in you, and that your joy may be made full.
Ina gaya maku wadannan al'amura domin farincikina ya kasance a cikin ku, kuma domin farincikinku ya zama cikakke.
12 “This is my commandment, that you love one another, even as I have loved you.
“Wannan shine umarnina, cewa ku kaunaci juna kamar yadda na kaunace ku.
13 Greater love has no one than this, that someone lay down his life for his friends.
Babu wanda ke da kaunar da tafi haka, wato ya bada ransa domin abokansa.
14 You are my friends if you do whatever I command you.
Ku abokaina ne idan kuna yin abubuwan da na umarce ku.
15 No longer do I call you servants, for the servant does not know what his lord does. But I have called you friends, for everything that I heard from my Father, I have made known to you.
Nan gaba ba zan kara ce da ku bayi ba, don bawa bai san abinda Ubangijinsa ke yi ba. Na kira ku abokaina, domin na sanar da ku duk abinda na ji daga wurin Ubana.
16 You did not choose me, but I chose you and appointed you, that you should go and bear fruit, and that your fruit should remain; that whatever you will ask of the Father in my name, he may give it to you.
Ba ku kuka zabe ni ba, amma Ni ne na zabe ku, na aike ku don ku je ku bada 'ya'ya, 'ya'yanku kuma su tabbata. Wannan ya zama domin duk abinda kuka roki Uba a cikin sunana, zai baku.
17 “I command these things to you, that you may love one another.
Na baku wannan umarni: domin ku kaunaci juna.
18 If the world hates you, you know that it has hated me before it hated you.
In duniya ta ki ku, ku sani cewa ta kini kafin ta ki ku.
19 If you were of the world, the world would love its own. But because you are not of the world, since I chose you out of the world, therefore the world hates you.
Da ku na duniya ne, da duniya ta kaunace ku kamar nata. Amma saboda ku ba na duniya bane, na kuma zabe ku daga duniya, don haka duniya take kin ku.
20 Remember the word that I said to you: ‘A servant is not greater than his lord.’ If they persecuted me, they will also persecute you. If they kept my word, they will also keep yours.
Ku tuna da maganar da na yi muku, 'Bawa ba ya fi Ubangijinsa girma ba.' Idan sun tsananta mani, ku ma za su tsananta maku; Idan sun kiyaye maganata, za su kuma kiyaye maganarku.
21 But they will do all these things to you for my name’s sake, because they do not know him who sent me.
Za su yi maku duk wadannan abubuwa saboda sunana, don basu san wanda ya aiko ni ba.
22 If I had not come and spoken to them, they would not have had sin; but now they have no excuse for their sin.
Da ban zo na yi masu magana ba, da basu da zunubi, amma yanzu, basu da wata hujja don zunubinsu.
23 He who hates me, hates my Father also.
Duk wanda ya ki ni ya ki Ubana.
24 If I had not done among them the works which no one else did, they would not have had sin. But now they have seen and also hated both me and my Father.
Da ban yi ayyukan da babu wanda ya taba yinsu a cikin su ba, da basu da zunubi, amma yanzu sun gani, sun kuma ki ni da Ubana duka.
25 But this happened so that the word may be fulfilled which was written in their law, ‘They hated me without a cause.’
An yi wannan kuwa domin a cika maganar da ke rubuce a cikin shari'arsu, ' Sun ki ni ba dalili.'
26 “When the Counselor has come, whom I will send to you from the Father, the Spirit of truth, who proceeds from the Father, he will testify about me.
Sa'adda Mai Ta'aziya- wanda zan aiko maku daga wurin Uban, wato, Ruhun gaskiya, wanda ke fita daga wurin Uban-ya zo, zai bada shaida a kai na.
27 You will also testify, because you have been with me from the beginning.
Ku ma kuna bada shaida saboda kuna tare da ni tun daga farko.

< John 15 >