< Genesis 8 >

1 God remembered Noah, all the animals, and all the livestock that were with him in the ship; and God made a wind to pass over the earth. The waters subsided.
Amma Allah ya tuna da Nuhu da dukan namun jeji da dabbobin da suke tare da shi a cikin jirgi, ya kuma aika da wata iska ta hura dukan duniya, ruwan kuwa ya janye.
2 The deep’s fountains and the sky’s windows were also stopped, and the rain from the sky was restrained.
Aka toshe maɓuɓɓugan zurfafa da ƙofofin ambaliyar sammai, ruwan sama kuma ya daina saukowa daga sarari.
3 The waters continually receded from the earth. After the end of one hundred fifty days the waters receded.
Ruwan ya janye a hankali daga ƙasa. A ƙarshen kwanaki ɗari da hamsin ɗin, ruwan ya ragu.
4 The ship rested in the seventh month, on the seventeenth day of the month, on Ararat’s mountains.
A rana ta goma sha bakwai ga watan bakwai, jirgin ya sauka a duwatsun Ararat.
5 The waters receded continually until the tenth month. In the tenth month, on the first day of the month, the tops of the mountains were visible.
Ruwan ya ci gaba da janyewa har watan goma. A rana ta fari ga watan goma kuwa ƙwanƙolin duwatsun suka bayyana.
6 At the end of forty days, Noah opened the window of the ship which he had made,
Bayan kwana arba’in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi,
7 and he sent out a raven. It went back and forth, until the waters were dried up from the earth.
ya saki hankaka. Hankaka ya yi ta kai da kawowa har sai da ruwa ya shanye a duniya.
8 He himself sent out a dove to see if the waters were abated from the surface of the ground,
Sai ya saki kurciya don yă ga in ruwan ya janye daga doron ƙasa.
9 but the dove found no place to rest her foot, and she returned into the ship to him, for the waters were on the surface of the whole earth. He put out his hand, and took her, and brought her to him into the ship.
Amma kurciyar ba tă sami inda za tă sa ƙafafunta ba gama akwai ruwa a dukan doron ƙasa, saboda haka ta komo wurin Nuhu a jirgi. Ya miƙa hannunsa ya ɗauko kurciyar ya shigar da ita wurinsa a cikin jirgi.
10 He waited yet another seven days; and again he sent the dove out of the ship.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar daga jirgi.
11 The dove came back to him at evening and, behold, in her mouth was a freshly plucked olive leaf. So Noah knew that the waters were abated from the earth.
Sa’ad da kurciya ta komo wurinsa da yamma, sai ga ɗanyen ganyen zaitun da ta tsinko a bakinta! Sa’an nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga duniya.
12 He waited yet another seven days, and sent out the dove; and she did not return to him any more.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar, amma a wannan ƙaro ba tă komo wurinsa ba.
13 In the six hundred first year, in the first month, the first day of the month, the waters were dried up from the earth. Noah removed the covering of the ship, and looked. He saw that the surface of the ground was dry.
A rana ta fari ga wata na fari wanda Nuhu ya cika shekaru 601, ruwa ya shanye a ƙasa. Sai Nuhu ya buɗe murfin jirgin, ya ga cewa doron ƙasa ya bushe.
14 In the second month, on the twenty-seventh day of the month, the earth was dry.
A ran ashirin da bakwai ga wata na biyu, ƙasa ta bushe ƙaƙaf.
15 God spoke to Noah, saying,
Sa’an nan Allah ya ce wa Nuhu,
16 “Go out of the ship, you, your wife, your sons, and your sons’ wives with you.
“Fito daga jirgin, kai da matarka da’ya’yanka maza da matansu.
17 Bring out with you every living thing that is with you of all flesh, including birds, livestock, and every creeping thing that creeps on the earth, that they may breed abundantly in the earth, and be fruitful, and multiply on the earth.”
Ka fitar da kowane iri halitta mai rai da take tare da kai waje, tsuntsaye, dabbobi, da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa, don su yi ta haihuwa, su yi yawa, su ƙaru a duniya.”
18 Noah went out, with his sons, his wife, and his sons’ wives with him.
Sai Nuhu ya fito tare da matarsa da’ya’yansa maza da matan’ya’yansa,
19 Every animal, every creeping thing, and every bird, whatever moves on the earth, after their families, went out of the ship.
da kowace irin dabba, da kowane mai rarrafe, da kowane irin tsuntsu, da kowane irin abu da yake tafiya a bisa duniya, suka fito daga jirgi daki-daki bisa ga irinsu.
20 Noah built an altar to the LORD, and took of every clean animal, and of every clean bird, and offered burnt offerings on the altar.
Sai Nuhu ya gina bagaden hadaya ga Ubangiji, ya ɗiba waɗansu dabbobi da tsuntsaye masu tsabta, ya yi hadaya ta ƙonawa da su a kan bagaden.
21 The LORD smelled the pleasant aroma. The LORD said in his heart, “I will not again curse the ground any more for man’s sake because the imagination of man’s heart is evil from his youth. I will never again strike every living thing, as I have done.
Da Ubangiji ya ji ƙanshi mai daɗi, sai ya ce a zuciyarsa, “Ba zan ƙara la’anta ƙasa saboda mutum ba, ko da yake dukan tunanin zuciyar mutum mugu ne tun yana ƙarami. Ba kuwa zan ƙara hallaka dukan halittu masu rai, kamar yadda na yi ba.
22 While the earth remains, seed time and harvest, and cold and heat, and summer and winter, and day and night will not cease.”
“Muddin duniya tana nan, lokacin shuki da na girbi, lokacin sanyi da na zafi, lokacin damina da na rani, dare da rana ba za su daina ba.”

< Genesis 8 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark