< Galatians 1 >

1 Paul, an apostle—not from men, nor through man, but through Jesus Christ, and God the Father, who raised him from the dead—
Bulus manzo, aikakke ba daga wurin mutum ba, ba kuma ta wurin mutane ba, amma ta wurin Yesu Kiristi da kuma Allah Uba, wanda ya tā da Yesu daga matattu.
2 and all the brothers who are with me, to the assemblies of Galatia:
Dukan’yan’uwan kuma da suke tare da ni a nan, Suna gai da ikkilisiyoyi a Galatiya.
3 Grace to you and peace from God the Father and our Lord Jesus Christ,
Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
4 who gave himself for our sins, that he might deliver us out of this present evil age (aiōn g165), according to the will of our God and Father—
Shi wanda ya ba da kansa saboda zunubanmu don yă cece mu daga wannan mugun zamani na yanzu, bisa ga nufin Allah wanda yake kuma Ubanmu, (aiōn g165)
5 to whom be the glory for the ages (aiōn g165) of the ages (aiōn g165). Amen.
a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn g165)
6 I marvel that you are so quickly deserting him who called you in the grace of Christ to a different “good news”,
Ina mamaki yadda kuka yi saurin yashe wanda ya kira ku ta wurin alherin Kiristi, kuna juyewa ga wata bishara dabam
7 but there is not another “good news.” Only there are some who trouble you and want to pervert the Good News of Christ.
wadda a gaskiya ba bishara ba ce ko kaɗan. Tabbatacce waɗansu mutane suna birkitar da ku, suna kuma ƙoƙari su karkatar da bisharar Kiristi.
8 But even though we, or an angel from heaven, should preach to you any “good news” other than that which we preached to you, let him be cursed.
Amma ko mu, ko mala’ika daga sama ya yi wa’azin wata bishara dabam da wadda muka yi muku, bari yă zama la’ananne har abada!
9 As we have said before, so I now say again: if any man preaches to you any “good news” other than that which you received, let him be cursed.
Kamar yadda muka riga muka faɗa, haka yanzu ma ina ƙara cewa in wani yana muku wa’azin wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, bari yă zama la’ananne har abada!
10 For am I now seeking the favor of men, or of God? Or am I striving to please men? For if I were still pleasing men, I would not be a servant of Christ.
Za a ce, ina ƙoƙarin neman amincewar mutane ne, ko amincewa ta Allah? Ko kuwa ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne? Da a ce har yanzu ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne, ai, da ban zama bawan Kiristi ba.
11 But I make known to you, brothers, concerning the Good News which was preached by me, that it is not according to man.
Ina so ku sani’yan’uwa, cewa bisharar da nake wa’azi, ba mutum ne ya ƙago ta ba.
12 For I did not receive it from man, nor was I taught it, but it came to me through revelation of Jesus Christ.
Ban karɓe ta daga wurin wani mutum ba, ba a kuma koya mini ita ba, a maimako, na karɓe ta, ta wurin wahayi daga Yesu Kiristi ne.
13 For you have heard of my way of living in time past in the Jews’ religion, how that beyond measure I persecuted the assembly of God and ravaged it.
Kun dai ji labarin rayuwata ta dā a cikin Yahudanci, yadda na tsananta wa ikkilisiyar Allah ƙwarai, na kuma yi ƙoƙarin hallaka ta.
14 I advanced in the Jews’ religion beyond many of my own age among my countrymen, being more exceedingly zealous for the traditions of my fathers.
Na ci gaba a cikin Yahudanci fiye da yawancin Yahudawan da suke tsarana, na kuma yi ƙwazo ƙwarai ga bin al’adun kakannina.
15 But when it was the good pleasure of God, who separated me from my mother’s womb and called me through his grace,
Amma sa’ad da Allah, wanda ya keɓe ni daga mahaifa ya kira ni ta wurin alherinsa, ya kuma gamshe shi
16 to reveal his Son in me, that I might preach him among the Gentiles, I did not immediately confer with flesh and blood,
yă bayyana Ɗansa a cikina, domin in yi wa’azinsa cikin Al’ummai. Ban nemi shawarar wani mutum ba.
17 nor did I go up to Jerusalem to those who were apostles before me, but I went away into Arabia. Then I returned to Damascus.
Ban kuma tafi Urushalima domin in ga waɗanda suka riga ni zaman manzanni ba, sai dai na hanzarta na tafi ƙasar Arabiya, daga baya sai na koma Damaskus.
18 Then after three years I went up to Jerusalem to visit Peter, and stayed with him fifteen days.
Bayan shekara uku, sai na haura zuwa Urushalima domin in sadu da Bitrus, na kuwa zauna tare da shi kwana goma sha biyar.
19 But of the other apostles I saw no one except James, the Lord’s brother.
Ban ga wani a ciki sauran manzanni ba, sai dai Yaƙub ɗan’uwan Ubangiji.
20 Now about the things which I write to you, behold, before God, I am not lying.
Ina tabbatar muku a gaban Allah cewa abin da nake rubuta muku ba ƙarya ba ne.
21 Then I came to the regions of Syria and Cilicia.
Daga baya sai na tafi Suriya da Silisiya.
22 I was still unknown by face to the assemblies of Judea which were in Christ,
Ikkilisiyoyin da suke cikin Kiristi da suke a Yahudiya ba su san ni ba tukuna.
23 but they only heard, “He who once persecuted us now preaches the faith that he once tried to destroy.”
Sun dai sami labari ne kawai cewa, “Mutumin da dā yake tsananta mana yanzu yana wa’azin bangaskiyar da dā ya yi ƙoƙari yă hallaka.”
24 So they glorified God in me.
Sai suka yabi Allah saboda ni.

< Galatians 1 >