< Ezekiel 29 >

1 In the tenth year, in the tenth month, on the twelfth day of the month, the LORD’s word came to me, saying,
A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, set your face against Pharaoh king of Egypt, and prophesy against him and against all Egypt.
“Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
3 Speak and say, ‘The Lord GOD says: “Behold, I am against you, Pharaoh king of Egypt, the great monster that lies in the middle of his rivers, that has said, ‘My river is my own, and I have made it for myself.’
Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
4 I will put hooks in your jaws, and I will make the fish of your rivers stick to your scales. I will bring you up out of the middle of your rivers, with all the fish of your rivers which stick to your scales.
Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
5 I will cast you out into the wilderness, you and all the fish of your rivers. You will fall on the open field. You will not be brought together or gathered. I have given you for food to the animals of the earth and to the birds of the sky.
Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
6 “‘“All the inhabitants of Egypt will know that I am the LORD, because they have been a staff of reed to the house of Israel.
Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
7 When they took hold of you by your hand, you broke and tore all their shoulders. When they leaned on you, you broke and paralyzed all of their thighs.”
Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
8 “‘Therefore the Lord GOD says: “Behold, I will bring a sword on you, and will cut off man and animal from you.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
9 The land of Egypt will be a desolation and a waste. Then they will know that I am the LORD. “‘“Because he has said, ‘The river is mine, and I have made it,’
Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
10 therefore, behold, I am against you and against your rivers. I will make the land of Egypt an utter waste and desolation, from the tower of Seveneh even to the border of Ethiopia.
saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
11 No foot of man will pass through it, nor will any animal foot pass through it. It will not be inhabited for forty years.
Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
12 I will make the land of Egypt a desolation in the middle of the countries that are desolate. Her cities among the cities that are laid waste will be a desolation forty years. I will scatter the Egyptians among the nations, and will disperse them through the countries.”
Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
13 “‘For the Lord GOD says: “At the end of forty years I will gather the Egyptians from the peoples where they were scattered.
“‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
14 I will reverse the captivity of Egypt, and will cause them to return into the land of Pathros, into the land of their birth. There they will be a lowly kingdom.
Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
15 It will be the lowest of the kingdoms. It will not lift itself up above the nations any more. I will diminish them so that they will no longer rule over the nations.
Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
16 It will no longer be the confidence of the house of Israel, bringing iniquity to memory, when they turn to look after them. Then they will know that I am the Lord GOD.”’”
Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
17 It came to pass in the twenty-seventh year, in the first month, in the first day of the month, the LORD’s word came to me, saying,
A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 “Son of man, Nebuchadnezzar king of Babylon caused his army to serve a great service against Tyre. Every head was made bald, and every shoulder was worn; yet he had no wages, nor did his army, from Tyre, for the service that he had served against it.
“Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
19 Therefore the Lord GOD says: ‘Behold, I will give the land of Egypt to Nebuchadnezzar king of Babylon. He will carry off her multitude, take her plunder, and take her prey. That will be the wages for his army.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
20 I have given him the land of Egypt as his payment for which he served, because they worked for me,’ says the Lord GOD.
Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 “In that day I will cause a horn to sprout for the house of Israel, and I will open your mouth among them. Then they will know that I am the LORD.”
“A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Ezekiel 29 >