< Exodus 40 >

1 The LORD spoke to Moses, saying,
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “On the first day of the first month you shall raise up the tabernacle of the Tent of Meeting.
“Ka kafa tabanakul, da Tentin Sujada, a kan rana ta fari ga watan fari.
3 You shall put the ark of the covenant in it, and you shall screen the ark with the veil.
Ka sa akwatin Alkawari a cikinsa, sa’an nan ka rufe shi da labule.
4 You shall bring in the table, and set in order the things that are on it. You shall bring in the lamp stand, and light its lamps.
Ka shigar da teburin ka shirya kayayyakin a kansa. Sa’an nan ka shigar da wurin ajiye fitilan ka kuma sa fitilunsa.
5 You shall set the golden altar for incense before the ark of the covenant, and put the screen of the door to the tabernacle.
Ka sa bagaden zinariya na ƙona turare a gaban akwatin Alkawari, ka kuma sa labule a ƙofar shiga tabanakul.
6 “You shall set the altar of burnt offering before the door of the tabernacle of the Tent of Meeting.
“Ka ajiye bagade na yin hadaya ta ƙonawa a gaban ƙofar tabanakul, da Tentin Sujada;
7 You shall set the basin between the Tent of Meeting and the altar, and shall put water therein.
ka ajiye daron tsakanin Tentin Sujada da bagaden, ka kuma zuba ruwa a cikinsa.
8 You shall set up the court around it, and hang up the screen of the gate of the court.
Ka yi fili kewaye da shi, ka kuma sa labule a ƙofar shiga filin.
9 “You shall take the anointing oil, and anoint the tabernacle and all that is in it, and shall make it holy, and all its furniture, and it will be holy.
“Ka ɗauki man shafewa ka shafe tabanakul da duka abin da yake cikinsa; ka keɓe shi da dukan kayayyakinsa, zai zama tsarkake.
10 You shall anoint the altar of burnt offering, with all its vessels, and sanctify the altar, and the altar will be most holy.
Sa’an nan ka shafe bagaden hadaya ta ƙonawa da kayansa; ka keɓe bagaden, zai zama mai tsarki.
11 You shall anoint the basin and its base, and sanctify it.
Ka shafe daron da wurin ajiyarsa, ka kuma keɓe su.
12 “You shall bring Aaron and his sons to the door of the Tent of Meeting, and shall wash them with water.
“Ka kawo Haruna da’ya’yansa a ƙofar Tentin Sujada ka wanke su da ruwa.
13 You shall put on Aaron the holy garments; and you shall anoint him, and sanctify him, that he may minister to me in the priest’s office.
Sa’an nan ka sa wa Haruna tsarkakun riguna, ka shafe shi, ka kuma keɓe shi don yă yi mini hidima a matsayin firist.
14 You shall bring his sons, and put tunics on them.
Ka kawo’ya’yansa maza ka sa musu taguwoyi.
15 You shall anoint them, as you anointed their father, that they may minister to me in the priest’s office. Their anointing shall be to them for an everlasting priesthood throughout their generations.”
Ka shafe su yadda ka shafe mahaifinsu, don su yi mini hidima a matsayin firistoci. Shafe musu man, zai sa su zama firistoci na ɗinɗinɗin, dukan zamanansu.”
16 Moses did so. According to all that the LORD commanded him, so he did.
Musa ya aikata dukan kome yadda Ubangiji ya umarce shi.
17 In the first month in the second year, on the first day of the month, the tabernacle was raised up.
Da haka aka kafa tabanakul, a rana ta fari ga wata na fari a shekara ta biyu.
18 Moses raised up the tabernacle, and laid its sockets, and set up its boards, and put in its bars, and raised up its pillars.
Sa’ad da Musa ya kafa tabanakul, ya sa rammuka a wurinsu, ya sa katakan, ya kuma sa sandunan, ya kakkafa dogayen sandunan.
19 He spread the covering over the tent, and put the roof of the tabernacle above on it, as the LORD commanded Moses.
Sa’an nan ya shimfiɗa tentin a bisa tabanakul, ya kuma sa murfi a bisa tentin, yadda Ubangiji ya umarce shi.
20 He took and put the covenant into the ark, and set the poles on the ark, and put the mercy seat above on the ark.
Ya ɗauki dokokin Alkawari ya sa a cikin akwatin, ya kuma zura sandunan a zoban akwatin, sa’an nan ya sa murfin kafara a bisansa.
21 He brought the ark into the tabernacle, and set up the veil of the screen, and screened the ark of the covenant, as the LORD commanded Moses.
Sai ya kawo akwatin a cikin tabanakul, ya kuma rataye labulen rufewa ya tsare akwatin Alkawarin, yadda Ubangiji ya umarce shi.
22 He put the table in the Tent of Meeting, on the north side of the tabernacle, outside of the veil.
Musa ya sa teburin a Tentin Sujada, a gefen arewa na tabanakul waje da labulen.
23 He set the bread in order on it before the LORD, as the LORD commanded Moses.
Ya shirya burodin a kai a gaban Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
24 He put the lamp stand in the Tent of Meeting, opposite the table, on the south side of the tabernacle.
Ya sa wurin ajiye fitilan a Tentin Sujada ɗaura da teburin a gefen kudu na tabanakul
25 He lit the lamps before the LORD, as the LORD commanded Moses.
ya kuma shirya fitilun a gaban Ubangiji, yadda Ubangiji ya umarce shi.
26 He put the golden altar in the Tent of Meeting before the veil;
Musa ya sa bagaden zinariya a cikin Tentin Sujada a gaban labulen
27 and he burned incense of sweet spices on it, as the LORD commanded Moses.
ya ƙone turare mai ƙanshi a kai, yadda Ubangiji ya umarce shi.
28 He put up the screen of the door to the tabernacle.
Sa’an nan ya sa labule a ƙofar shiga na tabanakul.
29 He set the altar of burnt offering at the door of the tabernacle of the Tent of Meeting, and offered on it the burnt offering and the meal offering, as the LORD commanded Moses.
Ya sa bagaden hadaya ta ƙonawa kusa da ƙofar tabanakul, Tentin Sujada, sa’an nan ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta gari a kansa, yadda Ubangiji ya umarce shi.
30 He set the basin between the Tent of Meeting and the altar, and put water therein, with which to wash.
Ya sa daro tsakanin Tentin Sujada da bagade, ya kuma zuba ruwa a cikinsa don wanki,
31 Moses, Aaron, and his sons washed their hands and their feet there.
a cikin kuwa Musa da Haruna da’ya’yansa maza sukan wanke hannunsa da ƙafafunsu.
32 When they went into the Tent of Meeting, and when they came near to the altar, they washed, as the LORD commanded Moses.
Sukan yi wanka a duk sa’ad da suka shiga Tentin Sujada, ko in suka kusaci bagade, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
33 He raised up the court around the tabernacle and the altar, and set up the screen of the gate of the court. So Moses finished the work.
Sa’an nan Musa ya yi fili kewaye da tabanakul da kuma bagaden, ya rataye labule a ƙofar shiga filin. Da haka Musa ya gama aikin.
34 Then the cloud covered the Tent of Meeting, and the LORD’s glory filled the tabernacle.
Sa’an nan girgije ya rufe Tentin Sujada sai ɗaukakar Ubangiji ta cika tabanakul.
35 Moses was not able to enter into the Tent of Meeting, because the cloud stayed on it, and the LORD’s glory filled the tabernacle.
Musa bai iya shiga Tentin Sujada ba domin girgije ya riga ya sauka a kansa, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika tabanakul.
36 When the cloud was taken up from over the tabernacle, the children of Israel went onward, throughout all their journeys;
Cikin tafiyar Isra’ilawa duka, sukan kama tafiyarsu ne a duk sa’ad da girgijen ya tashi daga kan tabanakul.
37 but if the cloud was not taken up, then they did not travel until the day that it was taken up.
Idan girgijen bai tashi ba, ba za su tashi ba, sai a ranar da ya tashi.
38 For the cloud of the LORD was on the tabernacle by day, and there was fire in the cloud by night, in the sight of all the house of Israel, throughout all their journeys.
Gama a cikin tafiyarsu duka, girgijen Ubangiji yana kan tabanakul da rana, da dare kuwa wuta yake cikinsa domin dukan Isra’ilawa su gani.

< Exodus 40 >