< Deuteronomy 14 >

1 You are the children of the LORD your God. You shall not cut yourselves, nor make any baldness between your eyes for the dead.
Ku’ya’yan Ubangiji Allahnku ne. Kada ku yi wa kanku zāne, ko ku yi wa kanku aski irin da akan bar sanƙo, saboda wanda ya mutu,
2 For you are a holy people to the LORD your God, and the LORD has chosen you to be a people for his own possession, above all peoples who are on the face of the earth.
gama ku jama’a ce mai tsarki ga Ubangiji Allahnku. Daga dukan mutane a fuskar duniya, Ubangiji ya zaɓe ku, ku zama abin mallakarsa.
3 You shall not eat any abominable thing.
Kada ku ci wani haramtaccen abu.
4 These are the animals which you may eat: the ox, the sheep, the goat,
Waɗannan su ne dabbobin da za ku iya ci, saniya, tunkiya, akuya,
5 the deer, the gazelle, the roebuck, the wild goat, the ibex, the antelope, and the chamois.
mariri, barewa, mariya, makwarna, mazo, gada da kuma tunkiyar dutse.
6 Every animal that parts the hoof, and has the hoof split in two and chews the cud, among the animals, you may eat.
Za ku iya cin duk dabbar da take da rababben kofato, wadda kuma take sāke tona abin da suka riga suka haɗiye.
7 Nevertheless these you shall not eat of them that chew the cud, or of those who have the hoof split: the camel, the hare, and the rabbit. Because they chew the cud but do not part the hoof, they are unclean to you.
Amma, cikin waɗanda suke sāke tona abin da suka riga suka haɗiye ɗin, ko suke da rababben kofato, ba za ku ci raƙumi, zomo ko rema ba. Ko da yake suna sāke tona abin da suka riga suka haɗiye, suna kuma da rababben kofato, su ɗin marar tsarki ne gare ku.
8 The pig, because it has a split hoof but does not chew the cud, is unclean to you. You shall not eat their meat. You shall not touch their carcasses.
Alade ma marar tsarki ne; ko da yake yana da rababben kofato, shi ba ya sāke tona abin da ya riga ya haɗiye. Ba za ku ci namansu ko ku taɓa gawarsu ba.
9 These you may eat of all that are in the waters: you may eat whatever has fins and scales.
Cikin dukan halittun da suke cikin ruwa, za ku iya cin duk wani da yake da ƙege da ɓamɓaroki.
10 You shall not eat whatever does not have fins and scales. It is unclean to you.
Amma duk wani abin da ba shi da ƙege da ɓamɓaroki, ba za ku ci ba; gama marar tsarki ne gare ku.
11 Of all clean birds you may eat.
Za ku iya cin kowane tsuntsu mai tsabta.
12 But these are they of which you shall not eat: the eagle, the vulture, the osprey,
Amma waɗannan ba za ku ci ba, gaggafa, ungulu, ungulun kwakwa,
13 the red kite, the falcon, the kite of any kind,
duki, buga zaɓi, kowace irin shirwa,
14 every raven of any kind,
kowane irin hankaka,
15 the ostrich, the owl, the seagull, the hawk of any kind,
jimina, ƙururu, bubuƙuwa, kowane irin shaho,
16 the little owl, the great owl, the horned owl,
da mujiya, da babbar mujiya, ɗuskwi,
17 the pelican, the vulture, the cormorant,
kwasakwasa, ungulu, da babba da jaka,
18 the stork, the heron after its kind, the hoopoe, and the bat.
zalɓe, kowane irin jinjimi, katutu, da kuma jamage.
19 All winged creeping things are unclean to you. They shall not be eaten.
Dukan’yan ƙwari masu fikafikai masu rarrafe, haram ne a gare ku, kada ku ci su.
20 Of all clean birds you may eat.
Amma duk wata halitta mai fikafikai mai tsabta ce, za ku iya ci.
21 You shall not eat of anything that dies of itself. You may give it to the foreigner living among you who is within your gates, that he may eat it; or you may sell it to a foreigner; for you are a holy people to the LORD your God. You shall not boil a young goat in its mother’s milk.
Kada ku ci abin da kun samu ya riga ya mutu. Za ku iya ba wa baren da yake zama a cikin wani daga biranenku, zai kuwa iya cinsa, ko kuwa za ku iya sayar da shi wa baƙo. Amma ku jama’a ce mai tsarki ga Ubangiji Allahnku. Kada ku dafa ɗan akuya a cikin madara mamansa.
22 You shall surely tithe all the increase of your seed, that which comes out of the field year by year.
Ku tabbata kun keɓe kashi ɗaya bisa goma na amfanin gonakinku kowace shekara.
23 You shall eat before the LORD your God, in the place which he chooses to cause his name to dwell, the tithe of your grain, of your new wine, and of your oil, and the firstborn of your herd and of your flock; that you may learn to fear the LORD your God always.
Ku ci zakkar hatsinku, da na sabon ruwan inabinku, da na manku, da kuma na’ya’yan fari na garkunanku na shanu da na tumaki a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da ya zaɓa a matsayin mazauni don Sunansa, don ku koyi girmama Ubangiji Allahnku kullum.
24 If the way is too long for you, so that you are not able to carry it because the place which the LORD your God shall choose to set his name there is too far from you, when the LORD your God blesses you,
Amma in wurin nan yana da nisa sosai, Ubangiji Allahnku kuma ya albarkace ku, ba za ku kuwa iya riƙe zakkarku ba (Saboda wurin da Ubangiji ya zaɓa yă sa Sunansa ya yi nisa sosai),
25 then you shall turn it into money, bind up the money in your hand, and shall go to the place which the LORD your God shall choose.
to, sai ku sayar da zakkar, ku tafi da kuɗin wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa.
26 You shall trade the money for whatever your soul desires: for cattle, or for sheep, or for wine, or for strong drink, or for whatever your soul asks of you. You shall eat there before the LORD your God, and you shall rejoice, you and your household.
Yi amfani da kuɗin ku saya duk abin da kuke so, ko shanu, ko tumaki, ko ruwan inabi, ko dai wani abin shan da ya yi tsami, ko kuwa duk abin da kuke so. Sai ku da gidanku, ku ci a can, a gaban Ubangiji Allahnku, ku kuma yi farin ciki.
27 You shall not forsake the Levite who is within your gates, for he has no portion nor inheritance with you.
Kada dai ku manta da Lawiyawan da suke zama a biranenku, gama ba su da rabo, ko gādo na kansu.
28 At the end of every three years you shall bring all the tithe of your increase in the same year, and shall store it within your gates.
A ƙarshen kowace shekara uku, ku kawo dukan zakkarku na amfanin gona na wannan shekara, ku ajiye su a cikin birane,
29 The Levite, because he has no portion nor inheritance with you, as well as the foreigner living among you, the fatherless, and the widow who are within your gates shall come, and shall eat and be satisfied; that the LORD your God may bless you in all the work of your hand which you do.
saboda Lawiyawa (waɗanda ba su da rabo ko gādo na kansu) da baƙo, da marayu, da kuma gwauraye, waɗanda suke zama a biranenku, su zo su ci su ƙoshi, ta haka Ubangiji Allahnku zai albarkace ku cikin dukan ayyukan hannuwanku.

< Deuteronomy 14 >