< 2 Samuel 22 >

1 David spoke to the LORD the words of this song in the day that the LORD delivered him out of the hand of all his enemies, and out of the hand of Saul,
Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
2 and he said: “The LORD is my rock, my fortress, and my deliverer, even mine;
Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
3 God is my rock in whom I take refuge; my shield, and the horn of my salvation, my high tower, and my refuge. My savior, you save me from violence.
Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
4 I call on the LORD, who is worthy to be praised; So shall I be saved from my enemies.
“Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
5 For the waves of death surrounded me. The floods of ungodliness made me afraid.
Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
6 The cords of Sheol (Sheol h7585) were around me. The snares of death caught me.
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol h7585)
7 In my distress, I called on the LORD. Yes, I called to my God. He heard my voice out of his temple. My cry came into his ears.
“A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
8 Then the earth shook and trembled. The foundations of heaven quaked and were shaken, because he was angry.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
9 Smoke went up out of his nostrils. Consuming fire came out of his mouth. Coals were kindled by it.
Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
10 He bowed the heavens also, and came down. Thick darkness was under his feet.
Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
11 He rode on a cherub, and flew. Yes, he was seen on the wings of the wind.
Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
12 He made darkness a shelter around himself, gathering of waters, and thick clouds of the skies.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
13 At the brightness before him, coals of fire were kindled.
Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
14 The LORD thundered from heaven. The Most High uttered his voice.
Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
15 He sent out arrows and scattered them, lightning and confused them.
Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
16 Then the channels of the sea appeared. The foundations of the world were laid bare by the LORD’s rebuke, at the blast of the breath of his nostrils.
Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
17 He sent from on high and he took me. He drew me out of many waters.
“Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
18 He delivered me from my strong enemy, from those who hated me, for they were too mighty for me.
Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
19 They came on me in the day of my calamity, but the LORD was my support.
Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
20 He also brought me out into a large place. He delivered me, because he delighted in me.
Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
21 The LORD rewarded me according to my righteousness. He rewarded me according to the cleanness of my hands.
“Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
22 For I have kept the LORD’s ways, and have not wickedly departed from my God.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
23 For all his ordinances were before me. As for his statutes, I did not depart from them.
Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
24 I was also perfect toward him. I kept myself from my iniquity.
Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
25 Therefore the LORD has rewarded me according to my righteousness, According to my cleanness in his eyesight.
Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
26 With the merciful you will show yourself merciful. With the perfect man you will show yourself perfect.
“Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
27 With the pure you will show yourself pure. With the crooked you will show yourself shrewd.
ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
28 You will save the afflicted people, but your eyes are on the arrogant, that you may bring them down.
Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
29 For you are my lamp, LORD. The LORD will light up my darkness.
Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
30 For by you, I run against a troop. By my God, I leap over a wall.
Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
31 As for God, his way is perfect. The LORD’s word is tested. He is a shield to all those who take refuge in him.
“Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
32 For who is God, besides the LORD? Who is a rock, besides our God?
Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
33 God is my strong fortress. He makes my way perfect.
Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
34 He makes his feet like hinds’ feet, and sets me on my high places.
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
35 He teaches my hands to war, so that my arms bend a bow of bronze.
Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
36 You have also given me the shield of your salvation. Your gentleness has made me great.
Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
37 You have enlarged my steps under me. My feet have not slipped.
Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
38 I have pursued my enemies and destroyed them. I did not turn again until they were consumed.
“Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
39 I have consumed them, and struck them through, so that they cannot arise. Yes, they have fallen under my feet.
Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
40 For you have armed me with strength for the battle. You have subdued under me those who rose up against me.
Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
41 You have also made my enemies turn their backs to me, that I might cut off those who hate me.
Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
42 They looked, but there was no one to save; even to the LORD, but he did not answer them.
Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
43 Then I beat them as small as the dust of the earth. I crushed them as the mire of the streets, and spread them abroad.
Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
44 You also have delivered me from the strivings of my people. You have kept me to be the head of the nations. A people whom I have not known will serve me.
“Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
45 The foreigners will submit themselves to me. As soon as they hear of me, they will obey me.
baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
46 The foreigners will fade away, and will come trembling out of their close places.
Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
47 The LORD lives! Blessed be my rock! Exalted be God, the rock of my salvation,
“Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
48 even the God who executes vengeance for me, who brings down peoples under me,
Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
49 who brings me away from my enemies. Yes, you lift me up above those who rise up against me. You deliver me from the violent man.
wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
50 Therefore I will give thanks to you, LORD, among the nations, and will sing praises to your name.
Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
51 He gives great deliverance to his king, and shows loving kindness to his anointed, to David and to his offspring, forever more.”
“Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”

< 2 Samuel 22 >